< 2 Rois 2 >
1 Lorsque Yahweh fit monter Elie au ciel dans un tourbillon, Elie s’en allait de Galgala avec Elisée.
Da lokaci ya yi da Ubangiji zai ɗauki Iliya zuwa sama cikin guguwa, Iliya da Elisha kuwa suna kan hanyarsu daga Gilgal.
2 Elie dit à Elisée: « Reste ici, je te prie, car Yahweh m’envoie jusqu’à Béthel. » Elisée répondit: « Yahweh est vivant et ton âme est vivante! Je ne te quitterai point! » Et ils descendirent à Béthel.
Sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ka dakata a nan; Ubangiji ya aike ni Betel.” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka gangara zuwa Betel.
3 Les fils des prophètes qui étaient à Béthel sortirent vers Elisée, et lui dirent: « Sais-tu que Yahweh enlèvera aujourd’hui ton maître de dessus ta tête? » Il répondit: « Je le sais aussi; tenez-vous en paix. »
Sai ƙungiyar annabawa a Betel suka fito zuwa wajen Elisha suka ce masa, “Ka san cewa Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga wurinka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma kada ku yi magana game da wannan.”
4 Elie lui dit: « Elisée, reste ici, je te prie, car Yahweh m’envoie à Jéricho. » Il répondit: « Yahweh est vivant et ton âme est vivante! Je ne te quitterai point! » Et ils arrivèrent à Jéricho.
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan Elisha; Ubangiji ya aike ni Yeriko.” Sai ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai ma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka sai suka tafi Yeriko.
5 Les fils des prophètes qui étaient à Jéricho s’approchèrent d’Elisée et lui dirent: « Sais-tu que Yahweh enlèvera aujourd’hui ton maître de dessus ta tête? » Il répondit: « Je le sais aussi; tenez-vous en paix. »
Ƙungiyar annabawa a Yeriko suka haura zuwa wajen Elisha suka ce, “Ko ka san Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga gare ka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma ku bar zancen nan tukuna.”
6 Elie lui dit: « Reste ici, je te prie, car Yahweh m’envoie au Jourdain. » Il répondit: « Yahweh est vivant et ton âme est vivante! Je ne te quitterai point! » Et ils s’en allèrent tous deux.
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan, Ubangiji ya aike ni Urdun.” Sai Elisha ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka ci gaba da tafiya tare.
7 Cinquante hommes d’entre les fils des prophètes allèrent après eux et se tinrent à distance, à l’opposé, et eux deux s’arrêtèrent au bord du Jourdain.
Mutum hamsin na ƙungiyar annabawa suka je suka tsaya da nisa, suna fuskantar inda Iliya da Elisha suka tsaya a Urdun.
8 Alors Elie, prenant son manteau, le roula et en frappa les eaux, qui se partagèrent d’un côté et de l’autre, et ils passèrent tous deux à sec.
Sai Iliya ya tuɓe rigarsa, ya nannaɗe ya bugi ruwan Urdun da shi. Sai ruwan ya dāre gida biyu, suka haye a busasshiyar ƙasa.
9 Lorsqu’ils eurent passé, Elie dit à Elisée: « Demande ce que tu veux que je fasse pour toi, avant que je sois enlevé d’avec toi. » Elisée répondit: « Que vienne sur moi une double portion de ton esprit? »
Da suka haye, sai Iliya ya ce wa Elisha, “Faɗi mini, abin da kake so in yi maka kafin a ɗauke ni daga gare ka!” Elisha ya amsa ya ce, “Bari in gāji ninki biyu na ruhunka.”
10 Elie dit: « Tu demandes une chose difficile. Si tu me vois pendant que je serai enlevé d’avec toi, il t’arrivera ainsi; sinon, cela n’arrivera pas. »
Iliya ya ce, “Ka nemi abu mai wuya, amma in ka ga lokacin da aka ɗauke ni daga gare ka, zai zama naka, in ba haka ba, ba za ka samu ba ke nan.”
11 Ils continuaient de marcher en s’entretenant, et voici qu’un char de feu et des chevaux de feu les séparèrent l’un de l’autre, et Elie monta au ciel dans un tourbillon.
Yayinda suke tafiya suna magana, sai kwatsam, keken yaƙin wuta da dawakan wuta suka ratse tsakaninsu, sai Iliya ya tafi sama a cikin guguwa.
12 Elisée regardait et criait: « Mon père! mon père! Char d’Israël et ses cavaliers! » Et il ne le vit plus. Il saisit alors ses vêtements et les déchira en deux morceaux,
Da Elisha ya ga haka sai ya yi ihu yana cewa, “Babana! Babana! Kekunan yaƙin da mahayan dawakan Isra’ila!” Elisha kuwa bai sāke ganinsa ba. Sai ya kama tufafinsa ya yayyage.
13 et il releva le manteau d’Elie qui était tombé de dessus lui. Puis, étant revenu au Jourdain, il s’arrêta sur le bord;
Sai ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya koma ya tsaya a gaɓar Kogin Urdun.
14 et, prenant le manteau d’Elie qui était tombé de dessus lui, il en frappa les eaux et dit: « Où est Yahweh, le Dieu d’Elie? Où est-il? » Lorsqu’il eut frappé les eaux, elles se partagèrent d’un côté et de l’autre, et Elisée passa.
Sa’an nan Elisha ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya bugi ruwan da shi. Ya ce, “Yanzu ina Ubangiji Allah na Iliya?” Da ya bugi ruwan sai ruwan ya dāre gida biyu, sai ya haye.
15 Les fils des prophètes qui étaient à Jéricho, à l’opposé, le virent et dirent: « L’esprit d’Elie repose sur Elisée; » et, allant à sa rencontre, ils se prosternèrent contre terre devant lui.
Ƙungiyar annabawa daga Yeriko, waɗanda suke kallo, suka ce, “Ruhun Iliya yana a kan Elisha.” Sai suka je su tarye shi, suka rusuna har ƙasa a gabansa.
16 Ils lui dirent: « Voici qu’il y a parmi tes serviteurs cinquante hommes vaillants: qu’ils aillent donc chercher ton maître. Peut-être que l’Esprit de Yahweh, l’ayant emporté, l’a jeté sur une des montagnes ou dans une des vallées. » Il répondit: « Ne les envoyez pas. »
Suka ce, “Duba, mu bayinka muna da masu ji da ƙarfi hamsin. Bari su je su nemi maigidanka. Wataƙila, Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi ya ajiye bisa wani dutse, ko wani kwari.” Elisha ya ce, “A’a, kada ku aike su.”
17 Mais ils le pressèrent jusqu’à le couvrir de confusion, et il leur dit: « Envoyez-les. » Ils envoyèrent cinquante hommes, qui cherchèrent Elie pendant trois jours, sans le trouver.
Amma suka matsa masa har ya ji ba ya iya hana su. Saboda haka ya ce, “Ku aike su.” Sai suka aiki mutane hamsin, suka yi ta nema har kwana uku amma ba su same Iliya ba.
18 Lorsqu’ils furent de retour auprès d’Elisée, — car il demeurait à Jéricho, — il leur dit: « Ne vous avais-je pas dit: N’allez pas? »
Da suka dawo wurin Elisha, wanda yake a Yeriko, sai ya ce musu, “Ban ce muku kada ku tafi ba?”
19 Les gens de la ville dirent à Elisée: « Le séjour de la ville est bon, comme le voit mon seigneur; mais les eaux sont mauvaises et le pays est stérile. »
Mutane garin suka ce wa Elisha, “Ranka yă daɗe, duba, garin yana da kyan gani, amma ruwan ba shi da kyau, ƙasar kuma ba ta ba da amfani.”
20 Il dit: « Apportez-moi une écuelle neuve, et mettez-y du sel. » Et ils la lui apportèrent.
Sai ya ce, “Ku kawo mini sabuwar ƙwarya, ku kuma sa gishiri a ciki.” Sai suka kawo masa.
21 Il alla vers la source des eaux et, y ayant jeté du sel, il dit: « Ainsi dit Yahweh: J’assainis ces eaux; il n’en proviendra plus ni mort, ni stérilité. »
Sai ya tafi maɓulɓular ruwan yana watsa gishirin a ciki, yana cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Na warkar da ruwan nan. Ba zai ƙara jawo mutuwa, ko yă hana ƙasar ba da amfani ba.’”
22 Et les eaux furent assainies jusqu’à ce jour, selon la parole qu’Elisée avait dite.
Ruwan ya tsabtacce har yă zuwa yau, bisa ga faɗin Elisha.
23 Il monta de là à Béthel; et comme il montait par la route, des petits garçons sortirent de la ville et se moquèrent de lui; ils lui disaient: « Monte, chauve! monte, chauve! »
Daga nan sai Elisha ya tafi Betel. Yayinda yake tafiya a hanya, sai waɗansu matasa suka fito daga cikin gari, suka yi masa dariya suna cewa, “Ka haura, ya kai mai kai marar gashi! Ka haura, kai mai kai marar gashi!”
24 Il se retourna pour les regarder, et il les maudit au nom de Yahweh. Et deux ours sortirent de la forêt et déchirèrent quarante-deux de ces enfants.
Sai ya juya ya dube su, ya la’anta su da sunan Ubangiji. Sai beyar guda biyu suka fito daga jeji suka hallaka matasa arba’in da biyu daga cikinsu.
25 De là il alla sur la montagne de Carmel, et de là il revint à Samarie.
Sai ya ci gaba zuwa Dutsen Karmel, daga can kuma ya koma Samariya.