< 2 Rois 18 >

1 La troisième année d’Osée, fils d’Ela, roi d’Israël, régna Ezéchias, fils d’Achaz, roi de Juda.
A shekara ta uku ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila, Hezekiya ɗan Ahaz sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Il avait vingt-cinq ans lorsqu’il devint roi, et il régna vingt-neuf ans à Jérusalem. Sa mère s’appelait Abi, fille de Zacharias.
Yana da shekara ashirin da biyar da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Abiya’yar Zakariya.
3 Il fit ce qui est droit aux yeux de Yahweh, selon tout ce qu’avait fait David, son père.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda kakansa Dawuda ya yi.
4 Il fit disparaître les hauts lieux, brisa les stèles, coupa les aschérahs, et mit en pièces le serpent d’airain que Moïse avait fait, car les enfants d’Israël brûlaient jusqu’alors des parfums devant lui: on l’appelait Nohestan.
Ya kawar da masujadan kan tudu, ya farfasa keɓaɓɓun duwatsu, ya sassare ginshiƙan Ashera. Ya fashe macijin tagullan da Musa ya yi, gama har zuwa lokacin nan Isra’ilawa suna ƙona turare gare shi. (An ba shi suna Nehushtan.)
5 Il mit sa confiance dans Yahweh, Dieu d’Israël, et il n’eut pas son semblable parmi tous les rois de Juda qui vinrent après lui ou qui le précédèrent.
Hezekiya ya dogara ga Ubangiji, Allah na Isra’ila. Ba a yi wani kamar sa ba cikin dukan sarakunan Yahuda; ko kafin shi, ko kuma bayansa.
6 Attaché à Yahweh, il ne se détourna pas de lui, et il observa ses commandements que Yahweh avait prescrits à Moïse.
Ya manne wa Ubangiji, bai fasa binsa ba; ya yi biyayya da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa.
7 Et Yahweh fut avec Ezéchias, et il réussit dans toutes ses entreprises. Ils se révolta contre le roi d’Assyrie, et il ne lui fut plus assujetti.
Ubangiji kuma ya kasance tare da shi, ya yi nasara a duk abin da ya sa hannu. Ya yi tawaye ga sarkin Assuriya, ya ƙi yă bauta masa.
8 Il battit les Philistins jusqu’à Gaza et ravagea son territoire, depuis la tour des gardiens jusqu’aux villes fortes.
Daga hasumiya zuwa birni mai katanga, ya ci Filistiyawa da yaƙi, har zuwa Gaza da kewaye.
9 La quatrième année du roi Ezéchias, qui était la septième année d’Osée, fils d’Ela, roi d’Israël, Salmanasar, roi d’Assyrie, monta contre Samarie et l’assiégea.
A shekara ta huɗu ta Hezekiya, wato, shekara ta bakwai ke nan ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila; Shalmaneser Sarkin Assuriya ya tasam ma Samariya da yaƙi; ya kewaye ta.
10 On la prit au bout de trois ans; ce fut la sixième année d’Ezéchias, qui était la neuvième d’Osée, roi d’Israël, que Samarie fut prise.
A ƙarshen shekara ta uku, Assuriyawa suka ci Samariya da yaƙi. An ci Samariya da yaƙi a shekara ta shida ta mulki Hezekiya, wanda ya zo daidai da shekara ta tara ta mulkin Hosheya sarkin Isra’ila.
11 Le roi d’Assyrie emmena Israël captif en Assyrie; il les établit à Hala, sur les rives du Habor, fleuve de Gosan, et dans les villes des Mèdes,
Sarkin Assuriya ya kwashe Isra’ila zuwa Assuriya ya zaunar da su a Hala, da Gozan a kogin Habor da kuma garuruwan Medes.
12 parce qu’ils n’avaient pas écouté la voix de Yahweh leur Dieu, et qu’ils avaient transgressé son alliance, parce qu’ils n’avaient ni écouté ni mis en pratique tout ce qu’avait ordonné Moïse, serviteur de Yahweh.
Wannan ya faru ne domin ba su yi biyayya ga Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsu; da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su saurari umarnin ba, balle su kiyaye su.
13 La quatorzième année du roi Ezéchias, Sennachérib, roi d’Assyrie, monta contre toutes les villes fortes de Juda et s’en empara.
A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin sarkin Hezekiya, sai sarki Sennakerib sarkin Assuriya ya kai farmaki wa biranen Yahuda masu katanga ya kuma kama su.
14 Ezéchias, roi de Juda, envoya dire au roi d’Assyrie à Lachis: « J’ai commis une faute; éloigne-toi de moi; ce que tu m’imposeras, je le subirai. » Et le roi d’Assyrie imposa à Ezéchias, roi de Juda, trois cents talents d’argent et trente talents d’or.
Sai Hezekiya sarkin Yahuda ya aika saƙo ga sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka janye daga gare ni, zan kuma biya ka duk abin da ake bukata daga gare ni.” Sarkin Assuriya ya karɓi talenti ɗari uku na azurfa, da talenti talatin na zinariya daga hannun Hezekiya sarkin Yahuda.
15 Ezéchias donna tout l’argent qui se trouvait dans la maison de Yahweh et dans les trésors de la maison du roi.
Ya zama kuwa cewa, Hezekiya ya bayar da dukan azurfan da suke a haikalin Ubangiji da kuma a ma’ajin fadan sarki.
16 En ce temps-là Ezéchias, roi de Juda, brisa les portes du temple de Yahweh et les piliers qu’Ezéchias, roi de Juda, avait lui-même revêtus d’or, et il donna l’or au roi d’Assyrie.
A wannan lokaci ne Hezekiya sarkin Yahuda ya ɓaɓɓalle zinariyan da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin haikalin Ubangiji, ya ba sarkin Assuriya.
17 Le roi d’Assyrie envoya de Lachis à Jérusalem, vers le roi Ezéchias, son général en chef, son chef des eunuques et son grand échanson avec une troupe nombreuse; ils montèrent et arrivèrent à Jérusalem. Lorsqu’ils furent montés et arrivés, ils s’arrêtèrent à l’aqueduc de l’étang supérieur, sur le chemin du champ du Foulon,
Sai sarkin Assuriya ya aika da babban shugaban sojojinsa, da shugaban dattawansa, da wakilinsa daga birnin Lakish tare da ƙungiyar sojoji masu yawa zuwa Urushalima domin su yaƙi Sarki Hezekiya. Da suka haura sai suka tsaya a wurin lambatun da yake kawo ruwa daga Tafkin Tudu, kusa da hanyar Filin Mai Wanki.
18 et appelèrent le roi. Eliacim, fils d’Helcias, chef de la maison du roi, se rendit auprès d’eux, avec Sobna, le secrétaire, et Joahé, fils d’Asaph, l’archiviste.
Suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka je wurinsu.
19 Le grand échanson leur dit: « Dites à Ezéchias: Ainsi dit le grand roi, le roi d’Assyrie: Quelle est cette confiance sur laquelle tu t’appuies?
Jagoran dogarawan sarkin Assuriya ya ce musu, “Ku ce wa Hezekiya, “‘Ga abin da babban sarkin Assuriya ya ce, da wa kake taƙama?
20 Tu as dit — paroles en l’air! — J’ai conseil et force pour la guerre. Et maintenant, en qui te confies-tu pour te révolter contre moi?
Ka ce kana da dabara da ƙarfin soji, amma bagu kawai kake yi. Da wa ka dogara har da za ka yi mini tawaye?
21 Voici que maintenant tu te fies à l’appui de ce roseau cassé — l’Égypte — qui pénètre et perce la main de quiconque s’appuie dessus: tel est Pharaon, roi d’Égypte, pour tous ceux qui se confient en lui.
Na sani kana dogara da Masar, wadda take kamar karar masara, wadda in ka jingina a kai, za tă karye tă soki hannunka. Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga dukan wanda ya dogara da shi.
22 Peut-être me direz-vous: C’est en Yahweh, notre Dieu, que nous avons confiance!... Mais n’est-ce pas lui dont Ezéchias a fait disparaître les hauts lieux et les autels, en disant à Juda et à Jérusalem: Vous vous prosternerez devant cet autel, à Jérusalem?
Sai ya ci gaba da cewa, in kuma ka ce mini “Muna dogara ga Ubangiji Allahnmu ne,” ba masujadansa da bagadansa ne Hezekiya ya ciccire, yana ce wa Urushalima da Yahuda, “Dole ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima”?
23 Maintenant, fais un accord avec mon maître, le roi d’Assyrie: je te donnerai deux mille chevaux, si tu peux fournir des cavaliers pour les monter!...
“‘Yanzu, ka zo ku shirya da shugabana, sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sami mahayansu!
24 Comment repousserais-tu un seul chef d’entre les moindres serviteurs de mon maître? Aussi mets-tu ta confiance dans l’Égypte pour les chars et pour les cavaliers.
Yaya za ka yi tsayayya da mafi ƙanƙantan hafsan shugabana, ko da kana dogara da Masar don kekunan yaƙi da mahaya dawakai?
25 Maintenant, est-ce sans la volonté de Yahweh que je suis monté contre ce lieu pour le détruire? Yahweh m’a dit: « Monte contre ce pays et détruis-le. »
Ban da haka ma, kana gani cewa na zo in hallaka wannan wuri ne ba tare da na ji daga Ubangiji ba? Ubangiji da kansa ne ya ce da ni in kawo wa wannan ƙasa hari in hallaka ta.’”
26 Eliacim, fils d’Helcias, Sobna et Joahé dirent au grand échanson: « Parle à tes serviteurs en araméen, car nous l’entendons; et ne nous parle pas en langue judaïque, aux oreilles du peuple qui est sur la muraille. »
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce wa jagoran dakarun, “Muna roƙonka ka yi wa bayinka magana da harshen Arameyik da yake muna ji. Kada ka yi mana magana da Yahudanci domin kada mutanen da suke bisa katanga su ji!”
27 Le grand échanson leur répondit: « Est-ce à ton maître et à toi que mon maître m’a envoyé dire ces paroles? N’est-ce pas à ces hommes assis sur la muraille, pour manger leurs excréments et pour boire leur urine avec vous? »
Amma shugaban sojojin ya ce, “Ai, ba gare ku da sarkinku kaɗai ne shugabana ya aike ni ba. Amma har ga mutanen da suke zaune a kan katangar birnin, waɗanda za su ci kashinsu, su sha fitsarinsu!”
28 Alors le grand échanson, s’étant avancé, cria à haute voix en langue judaïque et tint ce langage: « Ecoutez la parole du grand roi, du roi d’Assyrie!
Sai shugaban sojojin ya yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji muryar babban sarki, sarkin Assuriya!
29 Ainsi dit le roi: Qu’Ezéchias ne vous abuse pas, car il ne pourra vous délivrer de sa main.
Ga abin da sarki ya faɗa; kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku. Ba zai iya cetonku daga hannuna ba.
30 Qu’Ezéchias ne vous persuade pas de vous confier en Yahweh, en disant: Yahweh nous délivrera sûrement, et cette ville ne sera pas livrée entre les mains du roi d’Assyrie.
Kada ku yarda Hezekiya yă rinjaye ku cewa ku dogara ga Allah, sa’ad da ya ce da ku, ‘Ba shakka Ubangiji zai cece mu; yana ce da ku birnin nan ba zai faɗa a hannun sarkin Assuriya ba.’
31 N’écoutez pas Ezéchias, car ainsi dit le roi d’Assyrie: Faites la paix avec moi et rendez-vous à moi; et que chacun de vous mange de sa vigne et chacun de son figuier, et que chacun boive l’eau de son puits,
“Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya ce, ku shirya zaman lafiya da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci’ya’yan inabinsa da’ya’yan ɓaurensa, yă kuma sha ruwa daga randarsa,
32 jusqu’à ce que je vienne et que je vous emmène dans un pays comme le vôtre, un pays de blé et de vin, un pays de pain et de vignes, un pays d’oliviers à huile et de miel, afin que vous viviez et ne mourriez point. N’écoutez donc pas Ezéchias, car il vous abuse en disant: Yahweh nous délivrera.
har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi, da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! “Kada ku saurari Hezekiya, don karya yake muku, sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’
33 Est-ce que les dieux des nations ont délivré chacun leur pays de la main du roi d’Assyrie?
Akwai allahn wata al’ummar da ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
34 Où sont les dieux d’Emath et d’Arphad? Où sont les dieux de Sépharvaïm, d’Ana et d’Ava? Ont-ils délivré Samarie de ma main?
Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim, da na Hena, da na Iffa? Sun cece Samariya daga hannuna?
35 Quels sont, parmi tous les dieux des pays, ceux qui ont délivré leur pays de ma main, pour que Yahweh puisse délivrer Jérusalem de ma main? »
Wanne a cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa da gare ni? Shugaban sojojin ya kuma ci gaba da cewa, ta yaya Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?”
36 Le peuple se tut et ne lui répondit pas un mot, car le roi avait donné cet ordre: « Vous ne lui répondrez pas. »
Amma mutane suka yi shiru ba su amsa masa ba, domin sarki ya umarta cewa, “Kada ku amsa masa.”
37 Et Eliacim, fils d’Helcias, chef de la maison du roi, Sobna, le secrétaire, et Joahé, fils d’Asaph, l’archiviste, vinrent auprès d’Ezéchias, les vêtements déchirés, et lui rapportèrent les paroles du grand échanson.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf, marubuci, suka je wurin Hezekiya da tufafinsu a kece, suka faɗa masa abin da shugaban sojojin ya faɗa.

< 2 Rois 18 >