< 2 Rois 16 >

1 La dix-septième année de Phacée, fils de Romélias, régna Achaz, fils de Joatham, roi de Juda.
A shekara ta goma sha bakwai ta mulkin Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Achaz avait vingt ans lorsqu’il devint roi, et il régna seize ans à Jérusalem. Il ne fit pas ce qui est droit aux yeux de Yahweh, son Dieu, comme avait fait David, son père.
Ahaz ya zama sarki yana da shekara ashirin, ya kuma yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima ba kamar Dawuda mahaifinsa ba. Ahaz bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa ba.
3 Mais il marcha dans la voie des rois d’Israël, et même il fit passer son fils par le feu, selon les abominations des nations que Yahweh avait chassées devant les enfants d’Israël.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila har ya miƙa ɗansa hadaya a wuta, yana bin hanyoyin banƙyama na al’ummai da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 Il offrait des sacrifices et des parfums aux hauts lieux, sur les collines et sous tout arbre vert.
Ya miƙa hadaya, ya kuma ƙona turare a masujadan tudu, da kan tuddai, da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
5 Alors Rasin, roi de Syrie, et Phacée, fils de Romélias, roi d’Israël, montèrent contre Jérusalem pour l’attaquer. Ils assiégèrent Achaz, mais ils ne purent pas le vaincre.
Sai Rezin sarkin Aram, da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su kai wa Urushalima hari, suka kuma kewaye Ahaz, amma ba su iya shan ƙarfinsa ba.
6 Dans ce même temps, Rasin, roi de Syrie, ramena Elath au pouvoir des Syriens; il expulsa les Juifs d’Elath, et les Syriens vinrent à Elath, où ils ont habité jusqu’à ce jour.
A wannan lokaci, Rezin sarkin Aram ya sāke ƙwato Elat wa Aram ta wurin korar Yahuda. Sa’an nan mutanen Edom suka mamaye Elat suna kuwa zaune a can har yau.
7 Achaz envoya des messagers à Téglathphalasar, roi d’Assyrie, pour lui dire: « Je suis ton serviteur et ton fils; monte et délivre-moi de la main du roi de Syrie et de la main du roi d’Israël, qui se sont levés contre moi. »
Ahaz ya aika a faɗa wa Tiglat-Fileser sarkin Assuriya cewa, “Ni abokin tarayyarka ne kuma mai dogara da kai. Ka haura ka cece ni daga hannun sarkin Aram da hannun sarkin Isra’ila waɗanda suke kawo mini hari.”
8 Et Achaz prit l’argent et l’or qui se trouvaient dans la maison de Yahweh et dans les trésors de la maison du roi, et il l’envoya en présent au roi d’Assyrie.
Ahaz ya ɗauki azurfa da zinariyar da suke a haikalin Ubangiji da suke kuma a ma’ajin fada ya aika wa sarkin Assuriya kyauta.
9 Le roi d’Assyrie l’écouta, et le roi d’Assyrie monta contre Damas et, l’ayant prise, il en emmena les habitants en captivité à Qir, et il fit mourir Rasin.
Sai sarkin Assuriya ya ji roƙonsa. Ya tashi ya fāɗa wa Damaskus da hari ya kuma kame ta. Ya kwashi mazaunanta zuwa Kir, ya kuma kashe Rezin.
10 Le roi Achaz se rendit à Damas au-devant de Téglathphalasar, roi d’Assyrie. Ayant vu l’autel qui était à Damas, le roi Achaz envoya au prêtre Urias le modèle de l’autel et sa forme selon tout son travail.
Sa’an nan sarki Ahaz ya tafi Damaskus don yă sadu da Tiglat-Fileser sarkin Assuriya. Da ya kai can sai ya ga wani bagade a Damaskus, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayanin bagaden.
11 Le prêtre Urias construisit l’autel; le prêtre Urias le fit entièrement d’après le modèle que le roi Achaz avait envoyé de Damas, avant que le roi ne revienne de Damas.
Saboda haka Uriya firist ya gina bagaden bisa ga tsarin da Sarki Ahaz ya aika masa daga Damaskus, ya kuma gama shi kafin Sarki Ahaz yă dawo.
12 A son arrivée de Damas, le roi vit l’autel. Le roi s’approcha de l’autel et il y monta;
Da sarki ya dawo daga Damaskus ya ga bagaden, sai ya tafi kusa da shi ya kuma miƙa hadaya a bisansa.
13 il fit brûler son holocauste et son oblation, versa sa libation, et répandit sur l’autel le sang de ses sacrifices pacifiques.
Ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa da ta hatsi, ya zuba hadayarsa ta sha, ya kuma yayyafa jinin hadayunsa ta zumunci a bisa bagaden.
14 Il éloigna de devant la maison, d’entre le nouvel autel et la maison de Yahweh, l’autel d’airain qui était devant Yahweh, et il le plaça à côté du nouvel autel, vers le nord.
Sai ya cire bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi a gaban haikalin wato, tsakanin ƙofar shiga haikalin Ubangiji da sabon bagaden. Ya ajiye shi a gefen arewa na sabon bagaden.
15 le roi Achaz donna encore cet ordre au prêtre Urias: « Fais brûler sur le grand autel l’holocauste du matin et l’oblation du soir, l’holocauste du roi et son oblation, l’holocauste de tout le peuple du pays et leur oblation, verses-y leur libation et répands-y tout le sang des holocaustes et tout le sang des sacrifices. Pour ce qui concerne l’autel d’airain, il m’appartiendra d’y pourvoir. »
Sarkin Ahaz ya umarci Uriya cewa, “A kan babban sabon bagade, ka miƙa hadayar ƙonawa ta safe, da hadayar hatsi ta yamma, da hadayar sarki ta ƙonawa da hadayarsa ta hatsi, da hadaya ta dukan jama’ar ƙasar, tare da hadayan hatsinsu da kuma ta sha. Ka yayyafa jinin hadayun ƙonawa a kan bagade. Amma zan yi amfani da bagaden tagulla don neman bishewa.”
16 Le prêtre Urias fit tout ce qu’avait ordonné le roi Achaz.
Uriya firist kuwa ya yi duk abin da Sarki Ahaz ya umarta.
17 En outre, le roi Achaz brisa les cadres et les bases, et ôta les bassins qui étaient dessus; il descendit la mer d’airain de dessus les bœufs d’airain qui la supportaient, et il la posa sur un pavé de pierres;
Sarkin Ahaz ya kawar da katakon ya kuma ɗauke tasoshin daga mazauninsu da ake iya matsarwa. Ya ɗauke ƙaton kwano mai suna Teku daga kan bijiman tagullar da ya tallafe su ya ajiye a kan mazaunin dutse.
18 il changea, dans la maison de Yahweh, par considération pour le roi d’Assyrie, le portique du sabbat, qu’on avait construit dans la maison, et l’entrée extérieure du roi.
Ya kawar da rumfa Asabbacin da aka gina a haikalin, ya kuma kawar da mashigin sarki na waje da haikalin Ubangiji, duk dai don yă gamshi sarkin Assuriya.
19 Le reste des actes d’Achaz, et tout ce qu’il a fait, cela n’est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Ahaz, abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
20 Achaz se coucha avec ses pères, et il fut enterré avec ses pères dans la cité de David. Ezéchias, son fils, régna à sa place.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi da su a Birnin Dawuda. Hezekiya ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Rois 16 >