< 2 Rois 10 >

1 Il y avait dans Samarie soixante-dix fils d’Achab. Jéhu écrivit une lettre qu’il envoya à Samarie aux chefs de Jezrahel, les anciens, et aux gouverneurs des enfants d’Achab; il y disait:
To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
2 « Aussitôt que cette lettre vous sera parvenue, — puisque vous avez avec vous les fils de votre maître, avec vous les chars et les chevaux, une ville forte et les armes, —
“Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
3 voyez lequel des fils de votre maître est le meilleur et convient le mieux, mettez-le sur le trône de son père et combattez pour la maison de votre maître. »
sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
4 Ils eurent une très grande peur et ils dirent: « Voici que les deux rois n’ont pu lui résister; comment résisterions-nous? »
Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
5 Et le préfet du palais, le commandant de la ville, les anciens et les gouverneurs envoyèrent dire à Jéhu: « Nous sommes tes serviteurs et nous ferons tout ce que tu nous diras; nous n’établirons personne roi; fais ce qui te semblera bon. »
Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
6 Jéhu leur écrivit une seconde lettre; il disait: « Si vous êtes pour moi et si vous écoutez ma voix, prenez les têtes des hommes, fils de votre maître, et venez auprès de moi demain, à cette heure, à Jezrahel. » Or, les soixante-dix fils du roi étaient chez les grands de la ville, qui les élevaient.
Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
7 Quand la lettre leur fut parvenue, ils prirent les fils du roi et égorgèrent ces soixante-dix hommes; puis, ayant mis leurs têtes dans des corbeilles, ils les envoyèrent à Jéhu, à Jézrahel.
Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
8 Le messager vint l’en informer, en disant: « Ils ont apporté les têtes des fils du roi. » Et il dit: « Mettez-les en deux tas à l’entrée de la porte jusqu’au matin. »
Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
9 Le matin, il sortit et, se présentant à tout le peuple, il dit: « Vous êtes justes: voici que moi j’ai conspiré contre mon maître, et je l’ai tué; mais qui a frappé tous ceux-ci?
Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
10 Sachez donc qu’il ne tombe rien à terre de la parole de Yahweh, de la parole que Yahweh a prononcée sur la maison d’Achab; Yahweh a accompli ce qu’il a déclaré par l’organe de son serviteur Elie. »
Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
11 Et Jéhu frappa tous ceux qui restaient de la maison d’Achab à Jezrahel, tous ses grands, ses familiers et ses prêtres, jusqu’à ce qu’il n’en restât plus un seul.
Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
12 Puis, s’étant levé, il partit pour aller à Samarie. Arrivé à une maison de réunion des bergers, sur le chemin,
Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
13 Jéhu trouva les frères d’Ochozias, roi de Juda, et il dit: « Qui êtes-vous? » Ils répondirent: « Nous sommes les frères d’Ochozias, et nous descendons pour saluer les fils du roi et les fils de la reine. »
sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
14 Jéhu dit: « Saisissez-les vivants. » Et, les ayant saisis vivants, ils les égorgèrent à la citerne de la maison de réunion, au nombre de quarante-deux, sans que Jéhu en laissât échapper un seul.
Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
15 Etant parti de là, il rencontra Jonadab, fils de Réchab, qui venait au-devant de lui. Il le salua et lui dit: « Ton cœur est-il sincère, comme mon cœur l’est envers le tien? » Jonadab répondit: « Il l’est. » Et Jéhu dit: « S’il l’est, donne-moi ta main. » Il lui donna la main, et Jéhu le fit monter auprès de lui, dans le char,
Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
16 en disant: « Viens avec moi, et tu verras mon zèle pour Yahweh. » Il l’emmena ainsi sur son char.
Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
17 Arrivé à Samarie, Jéhu frappa tous ceux qui restaient à Samarie de la famille d’Achab, et il l’extermina, selon la parole que Yahweh avait dite à Elie.
Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
18 Jéhu assembla ensuite tout le peuple et leur dit: « Achab a peu servi Baal; Jéhu le servira beaucoup.
Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
19 Et maintenant, convoquez auprès de moi tous les prophètes de Baal, tous ses serviteurs et tous ses prêtres, sans qu’il en manque un seul, car j’ai un grand sacrifice à offrir à Baal; quiconque manquera ne vivra pas. » Or Jéhu agissait avec ruse, pour faire périr les serviteurs de Baal.
Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
20 Jéhu dit: « Publiez une assemblée solennelle en l’honneur de Baal »; et ils la publièrent.
Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
21 Jéhu envoya des messagers dans tout Israël, et tous les serviteurs de Baal vinrent, sans qu’un seul demeurât sans venir; ils entrèrent dans la maison de Baal, et la maison de Baal fut remplie d’un bout à l’autre.
Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
22 Jéhu dit à celui qui avait la garde du vestiaire: « Sorts des vêtements pour tous les serviteurs de Baal. » Et cet homme sortit des vêtements pour eux.
Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
23 Alors Jéhu, étant venu à la maison de Baal avec Jonadab, fils de Réchab, dit aux serviteurs de Baal: « Cherchez et regardez afin qu’il n’y ait ici avec nous aucun des serviteurs de Yahweh, mais seulement des serviteurs de Baal. »
Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
24 Lorsqu’ils furent entrés pour offrir des sacrifices et des holocaustes, Jéhu posta dehors quatre-vingts hommes, en leur disant: « Si quelqu’un des hommes que je mets entre vos mains s’échappe, la vie de celui qui l’aura laissé échapper paiera pour la sienne. »
Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
25 Aussitôt qu’il eut achevé d’offrir l’holocauste, Jéhu dit aux coureurs et aux officiers: « Entrez, frappez-les, que pas un ne sorte! » Et ils les frappèrent du tranchant de l’épée. Les coureurs et les officiers les jetèrent là, et, pénétrant dans le sanctuaire de la maison de Baal,
Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
26 ils tirèrent dehors les stèles de la maison de Baal et les brûlèrent;
suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
27 ils mirent en pièces la stèle de Baal; ils renversèrent aussi la maison de Baal et ils en firent un cloaque, qui a subsisté jusqu’à ce jour.
Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
28 Jéhu extermina Baal du milieu d’Israël.
Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
29 Mais Jéhu ne se détourna pas des péchés de Jéroboam, fils de Nabat, qui avait fait pécher Israël, ni des veaux d’or qui étaient à Béthel et qui étaient à Dan.
Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
30 Yahweh dit à Jéhu: « Parce que tu as bien exécuté ce qui était droit à mes yeux, et que tu as fait à la maison d’Achab tout ce qui était dans mon cœur, tes fils jusqu’à la quatrième génération seront assis sur le trône d’Israël. »
Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
31 Mais Jéhu ne prit pas garde à marcher de tout son cœur dans la loi de Yahweh, Dieu d’Israël; il ne se détourna pas des péchés de Jéroboam qui avait fait pécher Israël.
Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
32 En ces jours-là, Yahweh commença à retrancher du territoire d’Israël, et Hazaël battit les Israélites sur toute la frontière d’Israël;
A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
33 depuis le Jourdain, vers le soleil levant, il battit tout le pays de Galaad, les Gadites, les Rubénites, les Manassites, depuis Aroër, qui est sur le torrent de l’Arnon, jusqu’à Galaad et à Basan.
gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
34 Le reste des actes de Jéhu, tout ce qu’il a fait et tous ses exploits, cela n’est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois d’Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
35 Et Jéhu se coucha avec ses pères, et on l’enterra à Samarie. Joachaz, son fils, régna à sa place.
Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
36 Le temps que régna Jéhu sur Israël, à Samarie, fut de vingt-huit ans.
Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.

< 2 Rois 10 >