< 2 Corinthiens 11 >

1 Oh! si vous pouviez supporter de ma part un peu de folie! Mais oui, vous me supportez.
Ina fata za ku yi haƙuri da’yar wautata. Amma, ai, kun riga kun yi haƙuri.
2 J’ai conçu pour vous une jalousie de Dieu; car je vous ai fiancés à un époux unique, pour vous présenter au Christ comme une vierge pure.
Ina kishinku da kishi irin na Allah. Na yi muku alkawarin aure ga miji ɗaya, Kiristi, domin in miƙa ku a gare shi kamar budurwa zalla.
3 Mais je crains bien que, comme Eve fut séduite par l’astuce du serpent, ainsi vos pensées ne se corrompent et ne perdent leur simplicité à l’égard du Christ.
Sai dai ina tsoro kada yă zama, kamar yadda maciji ya yaudari Hawwa’u da makircinsa, ku ma a bauɗar da hankalinku daga sahihiyar biyayya amintacciya ga Kiristi.
4 Car si quelqu’un vient vous prêcher un autre Jésus que celui que nous vous avons prêché, ou si vous recevez un autre esprit que celui que vous avez reçu, ou un autre évangile que celui que vous avez embrassé, vous le supportez fort bien.
Gama in wani ya zo wurinku yana wa’azin wani Yesu dabam da wanda muka yi wa’azinsa, ko kuma in kun karɓi wani ruhu dabam da wanda kuka karɓa, ko wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, ya nuna kun yarda da su ke nan cikin sauƙinkai.
5 Certes, j’estime que je ne suis inférieur en rien à ces apôtres par excellence!
Amma a ganina waɗancan da kuke ce da su “manyan manzanni” ba su fi ni da wani abu ba.
6 Si je suis étranger à l’art de la parole, je ne le suis pas à la science; à tous égards et en tout, nous l’avons fait voir parmi vous.
Mai yiwuwa ni ba horarre ba ne a magana, amma ina da sani. Mun kuwa bayyana muku wannan a sarari, ta kowace hanya.
7 Ou bien ai-je commis une faute, parce qu’en m’abaissant moi-même pour vous élever, je vous ai annoncé gratuitement l’Evangile de Dieu?
Laifi ke nan ne na yi da na ƙasƙantar da kaina, don a ɗaga ku zuwa babban matsayi ta wurin yin muku wa’azin bisharar Allah kyauta?
8 J’ai dépouillé d’autres Eglises, en recevant d’elles un salaire, pour pouvoir vous servir.
Na yi wa waɗansu ikkilisiyoyi ƙwace ta wurin karɓar taimako daga wurinsu, domin in yi muku hidima.
9 Me trouvant au milieu de vous et dans le besoin, je n’ai été à charge à personne: des frères venus de Macédoine ont pourvu à ce qui me manquait. Je me suis gardé de vous être à charge en quoi que ce soit, et je m’en garderai.
Sa’ad da nake tare da ku kuma nake zaman rashi, ban nawaita wa kowa ba, gama’yan’uwan da suka zo daga Makidoniya sun biya bukata. Na kiyaye kaina daga nawaita muku ta kowace hanya, zan kuma ci gaba da yin haka.
10 Aussi vrai que la vérité du Christ est en moi, je proteste que cette gloire-là ne me sera pas les contrées de l’Achaïe.
Ba shakka, kamar yadda gaskiyar Kiristi take a cikina, babu wani a yankunan Akayya da zai iya hana yin taƙaman nan tawa.
11 Pourquoi? Parce que je ne vous aime pas? Ah! Dieu le sait!
Don me? Don ba na ƙaunar ku ne? Allah dai ya sani ina ƙaunarku!
12 Mais ce que je fais, je le ferai encore, pour ôter ce prétexte à ceux qui en cherchent un, afin d’être reconnus semblables à nous dans la conduite dont ils se vantent.
Zan kuma ci gaba da yin abin da nake yi, domin in toshe kafar mutanen nan da suke fariya, suna nema mu daidaita da su.
13 Ces gens-là sont de faux apôtres, des ouvriers astucieux, qui se déguisent en apôtres du Christ.
Gama irin waɗannan mutane manzannin ƙarya ne, ma’aikata ne masu ruɗi, sun ɓad da kamanni kamar su manzannin Kiristi ne.
14 Et ne vous en étonnez pas; car Satan lui-même se déguise en ange de lumière.
Ba abin mamaki ba ne, gama Shaiɗan kansa ma yana ɓad da kamanni kamar shi mala’ikan haske ne.
15 Il n’est donc pas étrange que ses ministres aussi se déguisent en ministres de justice. Leur fin sera selon leurs œuvres.
Don haka, ba abin mamaki ba ne, in bayin Shaiɗan sun ɓad da kamanni kamar su bayin adalci ne. A ƙarshe, za a sāka musu gwargwadon ayyukansu.
16 Je le répète, que personne ne me regarde comme un insensé; si non, acceptez-moi comme tel, afin que moi aussi je me glorifie un peu.
Ina sāke faɗa, kada wani yă ɗauka ni wawa ne. Amma in kun ɗauke ni haka, to, sai ku karɓe ni kamar yadda kuke karɓan wawa, domin in ɗan in yi taƙama.
17 Ce que je vais dire, avec cette assurance d’avoir sujet de me glorifier, je ne le dis pas selon le Seigneur, mais comme si j’étais en état de folie.
A wannan taƙamata ba na magana yadda Ubangiji zai yi ba ne, sai dai magana ce irin ta wawa.
18 Puisque tant de gens se glorifient selon la chair, je me glorifierai aussi.
Da yake mutane da yawa suna taƙama irin ta duniya, ni ma haka zan yi.
19 Et vous qui êtes sensés, vous supportez volontiers les insensés.
Ku kam kuna da wayo sosai, har kuna jimre wa wawaye da murna!
20 Vous supportez bien qu’on vous asservisse, qu’on vous dévore, qu’on vous pille, qu’on vous traite avec arrogance, qu’on vous frappe au visage.
Gaskiyar ita ce, kuna haƙuri da duk wanda ya sa ku bauta ko ya cuce ku ko ya more ku ko ya nuna muku isa ko kuma ya mare ku a fuska.
21 Je le dis à ma honte, nous avons été bien faibles! Cependant, de quoi que ce soit qu’on ose se vanter, — je parle en insensé, moi aussi je l’ose.
Ina jin kunya in ce mun nuna kāsawa da ba mu yi waɗannan abubuwan ba! Abin da wani yake da ƙarfin hali yin taƙama a kai, shi ne ni ma nake ƙarfin hali yin taƙama a kai. Ina magana kamar wawa ne.
22 Sont-ils Hébreux? Moi aussi, je le suis. Sont-ils Israélites? Moi aussi. Sont-ils de la postérité d’Abraham? Moi aussi.
In su Ibraniyawa ne, ni ma haka. In su Isra’ilawa ne, ni ma haka. In su zuriyar Ibrahim ne, ni ma haka.
23 Sont-ils ministres du Christ? — Ah! je vais parler en homme hors de sens: — je le suis plus qu’eux: bien plus qu’eux par les travaux, bien plus par les coups, infiniment plus par les emprisonnements; souvent j’ai vu de près la mort;
In su bayin Kiristi ne, ni na fi su ma, ina magana kamar ruɗaɗɗe ne fa! Ai, na fi su shan fama ƙwarai da gaske, da shan dauri, na sha dūka marar iyaka, na sha hatsarin mutuwa iri-iri.
24 cinq fois j’ai reçu des Juifs quarante coups de fouet moins un;
Sau biyar Yahudawa suka yi mini bulala arba’in ɗaya babu.
25 trois fois, j’ai été battu de verges; une fois j’ai été lapidé; trois fois j’ai fait naufrage; j’ai passé un jour et une nuit dans l’abîme.
Sau uku aka bulale ni da bulalar ƙarfe, sau ɗaya aka jajjefe ni da duwatsu, sau uku jirgin ruwa ya ragargaje ina ciki, na kwana na kuma yini ruwan teku yana tafiya da ni.
26 Et mes voyages sans nombre, les périls sur les fleuves, les périls de la part des brigands, les périls de la part de ceux de ma nation, les périls de la part des Gentils, les périls dans les villes, les périls dans les déserts, les périls sur la mer, les périls de la part des faux frères,
Na yi tafiye-tafiye da yawa, na sha hatsari a koguna, na sha hatsarin’yan fashi, na sha hatsari a hannun kabilarmu, na sha hatsari a hannun al’ummai, na sha hatsari a birane, na sha hatsari a jeji, na sha hatsari a teku, na kuma sha hatsarin’yan’uwa na ƙarya.
27 les labeurs et les peines, les nombreuses veilles, la faim, la soif, les jeûnes multipliés, le froid, la nudité!
Na yi fama, na shan wuya, ga kuma rashin barci sau da yawa. Na san abin da ake nufin da jin yunwa da ƙishirwa, sau da yawa kuwa na kasance da rashin abinci, na sha sanyi da zaman tsirara.
28 Et sans parler de tant d’autres choses, rappellerai-je mes soucis de chaque jour, la sollicitude de toutes les Eglises?
Ban da waɗannan abubuwa, kowace rana ina ɗauke da nauyin kula da dukan ikkilisiyoyi.
29 Qui est faible que je ne sois faible aussi? Qui vient à tomber sans qu’un feu me dévore?
Wane ne ya rasa ƙarfi, da ban ji shi a jikina ba? Wane ne ya fāɗi cikin zunubi, da ban ji zafin wannan ba?
30 S’il faut se glorifier, c’est de ma faiblesse que je me glorifierai.
In ma lalle ne in yi taƙama, to, sai in yi taƙama da abubuwan da suka nuna rashin ƙarfina.
31 Dieu, qui est le Père de notre Seigneur Jésus-Christ, et qui est béni éternellement, sait que je ne mens pas. (aiōn g165)
Allah Uban Ubangiji Yesu Kiristi, wanda yabo ta tabbata a gare shi har abada, ya san cewa ba ƙarya nake yi ba. (aiōn g165)
32 A Damas, l’ethnarque du roi Arétas faisait garder la ville pour se saisir de moi;
A Damaskus, gwamnan da yake ƙarƙashin Sarki Aretas, ya sa tsare ƙofofin birnin Damaskus, don yă kama ni.
33 mais on me descendit par une fenêtre, dans une corbeille, le long de la muraille, et j’échappai ainsi de ses mains.
Amma aka saukar da ni cikin kwando ta tagar katanga, na kuɓuce masa.

< 2 Corinthiens 11 >