< 2 Chroniques 6 >

1 Alors Salomon dit: « Yahweh veut habiter dans l’obscurité!
Sa’an nan Solomon ya ce, “Ubangiji ya faɗa cewa zai zauna cikin duhun girgije;
2 Et moi j’ai bâti une maison qui sera votre demeure, et un lieu pour que vous y résidiez à jamais. »
na gina ƙasaitaccen haikali dominka, wuri domin ka zauna har abada.”
3 Puis le roi tourna son visage et bénit toute l’assemblée d’Israël, et toute l’assemblée d’Israël était debout.
Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
4 Et il dit: « Béni soit Yahweh, Dieu d’Israël, qui a parlé par sa bouche à David, mon père, et qui a accompli par ses mains ce qu’il avait déclaré, en disant:
Sa’an nan ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannuwansa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
5 Depuis le jour où j’ai fait sortir du pays d’Égypte mon peuple, je n’ai pas choisi de ville, parmi toutes les tribus d’Israël, pour qu’on y bâtisse une maison où réside mon nom, et je n’ai pas choisi d’homme pour qu’il fût chef de mon peuple d’Israël;
‘Tun ranar na da fitar da mutanena daga Masar, ban zaɓi wani birni a wata kabilar Isra’ila don a gina haikali domin Sunana ya kasance a can ba, ba kuwa zaɓi wani yă zama shugaba a bisa jama’ata Isra’ila ba.
6 mais j’ai choisi Jérusalem pour que mon nom y réside, et j’ai choisi David pour qu’il règne sur mon peuple d’Israël.
Amma yanzu na zaɓi Urushalima domin Sunana yă kasance a can, na kuma zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
7 David, mon père, avait l’intention de bâtir une maison au nom de Yahweh, Dieu d’Israël;
“Mahaifina Dawuda ya yi niyya a zuciyarsa yă gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
8 mais Yahweh dit à David, mon père: Puisque tu as l’intention de bâtir une maison à mon nom, tu as bien fait d’avoir eu cette intention.
Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Domin yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka kasance da wannan a zuciyarka.
9 Seulement ce ne sera pas toi qui bâtiras la maison; ce sera ton fils, sorti de tes entrailles, qui bâtira la maison à mon nom.
Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikalin, amma ɗanka wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
10 Yahweh a accompli la parole qu’il avait prononcée: je me suis élevé à la place de David, mon père, et je me suis assis sur le trône d’Israël, comme Yahweh l’avait dit, et j’ai bâti la maison de Yahweh, Dieu d’Israël.
“Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina yanzu kuwa na zauna a kan kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya alkawarta, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
11 Et j’y ai placé l’arche où se trouve l’alliance de Yahweh, alliance qu’il a faite avec les enfants d’Israël. »
A can na ajiye akwatin alkawari, inda alkawarin Ubangiji da ya yi da mutanen Isra’ila yake.”
12 Salomon se plaça devant l’autel de Yahweh, en face de toute l’assemblée d’Israël, et il étendit ses mains.
Sa’an nan Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji a gaban dukan taron Isra’ila ya ɗaga hannuwansa sama.
13 Car Salomon avait fait une tribune d’airain et l’avait dressée au milieu du parvis; sa longueur était de cinq coudées, sa largeur de cinq coudées, et sa hauteur de trois coudées. Il y monta et, s’étant mis à genoux en face de toute l’assemblée d’Israël, il étendit ses mains vers le ciel,
Dā ma ya riga ya gina dakalin tagulla, mai tsawo kamu biyar, fāɗi kamu biyar da kuma tsayi kamu uku, ya kuma sa shi a tsakiyar filin waje. Ya tsaya a kan dakalin ya kuma durƙusa a gaban dukan taron Isra’ila ya buɗe hannuwansa sama.
14 et dit: « Yahweh, Dieu d’Israël, il n’y a pas de Dieu semblable à vous dans les cieux et sur la terre; à vous, qui gardez l’alliance et la miséricorde envers vos serviteurs qui marchent de tout leur cœur en votre présence;
Ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama da kuma ƙasa, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna tare da bayinka waɗanda suke cin gaba da zuciya ɗaya a hanyarka.
15 comme vous avez gardé à votre serviteur David, mon père, ce que vous lui avez dit; ce que vous avez déclaré de votre bouche, vous l’avez accompli par votre main, comme on le voit en ce jour.
Ka kiyaye alkawarinka ga bawanka Dawuda mahaifina; da bakinka ka yi alkawari kuma da hannunka ka cika shi, yadda yake a yau.
16 Maintenant, Yahweh, Dieu d’Israël, observez, en faveur de votre serviteur David, mon père, ce que vous lui avez dit, en ces termes: « Il ne te manquera jamais devant moi un descendant qui siège sur le trône d’Israël, pourvu que tes fils prennent garde à leur voie, en marchant dans ma loi comme tu as marché devant moi.
“Yanzu fa Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka kiyaye wa bawanka Dawuda mahaifina alkawuran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka kāsa kasance da mutumin da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza za su kula cikin dukan abin da suke yi su yi tafiya a gabana bisa ga dokata, kamar yadda ka yi.’
17 Et maintenant, Yahweh, Dieu d’Israël, qu’elle s’accomplisse la parole que vous avez dite à votre serviteur David!
Yanzu kuwa, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi alkawarta wa bawanka Dawuda yă cika.
18 Mais est-il donc vrai que Dieu habite avec l’homme sur la terre? Voici que le ciel et le ciel des cieux ne peuvent vous contenir: combien moins cette maison que j’ai bâtie?
“Amma tabbatacce Allah zai zauna a duniya tare da mutane? Sammai, har ma da saman sammai, ba za su iya riƙe ka ba. Balle wannan haikalin da na gina!
19 Cependant, Yahweh, mon Dieu, soyez attentif à la prière de votre serviteur et à sa supplication, en écoutant le cri joyeux et la prière que votre serviteur prononce devant vous,
Duk da haka ka mai da hankali ga addu’ar bawanka da kuma roƙo don jinƙai, ya Ubangiji, Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka.
20 en tenant vos yeux ouverts jour et nuit sur cette maison, sur le lieu dont vous avec dit que vous mettriez là votre nom, en écoutant la prière que votre serviteur fait en ce lieu.
Bari idanunka su buɗu ta wajen wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce za ka sa Sunanka a can. Bari ka ji addu’ar da bawanka ke yi ta wajen wannan wuri.
21 Ecoutez les supplications de votre serviteur et de votre peuple d’Israël, lorsqu’ils prieront en ce lieu. Ecoutez du lieu de votre demeure, du ciel, écoutez et pardonnez.
Ka ji roƙe-roƙen bawanka da na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a suna duban wajen wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka; kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
22 Si quelqu’un pèche contre son prochain, et qu’on lui fasse prêter un serment, s’il vient jurer devant votre autel, dans cette maison,
“Sa’ad da mutum ya yi wa maƙwabcinsa laifi aka kuma bukaci ya yi rantsuwa, ya kuma zo ya rantse a gaban bagadenka a cikin wannan haikali,
23 écoutez-le du ciel, agissez, et jugez vos serviteurs, condamnant le coupable et faisant retomber sa conduite sur sa tête, déclarant juste l’innocent, et lui rendant selon son innocence.
sai ka ji daga sama ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, kana sāka wa mai laifi ta wurin kawo a kansa hakkin abin da ya yi. Ka nuna cewa marar laifi ba shi da laifi, ta haka a fiffita rashin laifinsa.
24 Quand votre peuple d’Israël sera battu devant l’ennemi, parce qu’il aura péché contre vous, s’ils reviennent et rendent gloire à votre nom, s’ils vous adressent des prières et des supplications dans cette maison,
“Sa’ad da an ci mutanenka Isra’ila a yaƙi ta wurin abokin gāba domin sun yi maka zunubi kuma sa’ad da suka juya suka furta sunanka, suna addu’a suka kuma yin roƙe-roƙe a gabanka a wannan haikali,
25 écoutez-les du ciel, pardonnez le péché de votre peuple d’Israël, et ramenez-les dans le pays que vous leur avez donné, à eux et à leurs pères.
sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin mutanenka Isra’ila ka kuma dawo da su zuwa ƙasar da ka ba su da kuma kakanninsu.
26 Quand le ciel sera fermé et qu’il n’y aura pas de pluie, parce qu’ils auront péché contre vous, s’ils prient dans ce lieu et rendent gloire à votre nom, et s’ils se détournent de leurs péchés, parce que vous les aurez affligés,
“Sa’ad da sammai suka rufu ba kuwa ruwan sama saboda mutanenka sun yi maka zunubi, sa’ad da kuwa suka yi addu’a suna duban waje wannan wuri suka kuma furta sunanka suka juye daga zunubinsu domin ka azabta su,
27 écoutez-les du ciel, pardonnez les péchés de vos serviteurs et de votre peuple d’Israël, en leur enseignant la bonne voie dans laquelle ils doivent marcher, et faites tomber la pluie sur la terre que vous avez donnée pour héritage à votre peuple.
sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace da za su yi zama, ka kuma aika ruwan sama a ƙasar da ka ba mutanenka gādo.
28 Quand la famine sera dans le pays, quand il y aura la peste, quand il y aura la rouille, la nielle, la sauterelle, le hasil; quand l’ennemi assiégera votre peuple dans le pays, dans ses portes, quand il y aura fléau et maladie quelconques,
“Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko wahala ko fumfuna, ko fāra ko fāra ɗango, ko sa’ad da abokan gāba sun yi musu ƙawanya a kowane daga biranensu, dukan wata masifa ko cutar da za tă zo,
29 si un homme, si tout votre peuple d’Israël fait entendre des prières et des supplications, et que chacun, reconnaissant sa plaie et sa douleur, étende ses mains vers cette maison,
sa’ad da kuwa wani cikin mutanenka Isra’ila ya yi wata addu’a ko roƙo, kowa yana sane a azabarsa da kuma zafinsa, yana buɗe hannuwansa yana duban wajen wannan haikali,
30 écoutez-le du ciel, du lieu de votre demeure, et pardonnez; rendez à chacun selon toutes ses voies, vous qui connaissez son cœur, — car seul vous connaissez les cœurs des enfants des hommes, —
sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi da kowane mutum gwargwadon duk abin da yake yi, da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan mutane),
31 afin qu’ils vous craignent en marchant dans vos voies, tous les jours qu’ils vivront sur la face du pays que vous avez donné à leurs pères.
don su ji tsoronka su kuma yi tafiya a hanyoyinka a kowane lokacin da suke zama a ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
32 Quant à l’étranger, qui n’est pas de votre peuple d’Israël, mais qui viendra d’un pays lointain à cause de votre grand nom, de votre main forte et de votre bras étendu, quand il viendra prier dans cette maison,
“Game da baƙo wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba kuwa amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka mai girma da kuma hannunka mai iko da hannunka mai ƙarfi, sa’ad da ya zo ya yi addu’a yana duban wannan haikali,
33 écoutez-le du ciel, du lieu de votre demeure, et agissez selon tout ce que vous demandera l’étranger, afin que tous les peuples de la terre connaissent votre nom, pour vous craindre, comme votre peuple d’Israël, et qu’ils sachent que votre nom est appelé sur cette maison que j’ai bâtie.
sai ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi duk abin da baƙon ya nemi ka yi, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, su kuma san cewa wannan gidan da na gina na Sunanka ne.
34 Quand votre peuple sortira pour combattre son ennemi, en suivant la voie dans laquelle vous les aurez envoyés, s’ils vous adressent des prières, le visage tourné vers cette ville que vous avez choisie et vers la maison que j’ai bâtie à votre nom,
“Sa’ad da mutanenka suka je yaƙi da abokan gābansu, ko’ina ka kai su, kuma sa’ad da suka yi addu’a gare ka suna duban wannan birnin da ka zaɓa da haikalin nan da na gina domin Sunanka,
35 écoutez du ciel leur prière et leur supplication, et rendez-leur justice.
sai ka ji addu’arsu da kuma roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatarsu.
36 Quand ils pécheront contre vous — car il n’y a pas d’homme qui ne pèche, — et quand, irrité contre eux, vous les livrerez à l’ennemi, et que leur vainqueur les emmènera captifs dans un pays lointain ou rapproché,
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wani wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su ka miƙa su ga abokin gāba, wanda ya kai su zaman bauta a ƙasa mai nisa ko kuwa kusa;
37 s’ils rentrent en eux-mêmes dans le pays où ils seront captifs, s’ils reviennent à vous et vous adressent des supplications dans le pays de leur captivité, en disant: Nous avons péché, nous avons fait l’iniquité, nous avons commis le crime;
Kuma in suka canja zuciya a cikin ƙasar da suke zaman bauta, suka tuba suka roƙe ka a ƙasar zaman bautarsu suka kuma ce, ‘Mun yi zunubi, mu yi abin da ba daidai ba, mu kuwa yi mugunta’;
38 s’ils reviennent à vous de tout leur cœur et de toute leur âme, dans le pays de leur captivité où on les aura emmenés captifs, s’ils vous adressent des prières le visage tourné vers le pays que vous avez donné à leurs pères, vers la ville que vous avez choisie et vers la maison que j’ai bâtie à votre nom,
in kuma sun juye gare ka da dukan zuciyarsu da ransu a ƙasar zaman bautarsu inda aka kai su, suka kuma dubi wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, wajen birnin da ka zaɓa da kuma wajen haikalin da na gina domin Sunanka;
39 écoutez du ciel, du lieu de votre demeure, leur prière et leur supplication, et faites-leur droit, et pardonnez à votre peuple ses transgressions contre vous.
to, daga sama, mazauninka, sai ka ji addu’arsu da kuma roƙe-roƙensu, ka kuwa biya musu bukatunsu. Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi.
40 Maintenant, ô mon Dieu, que vos yeux soient ouverts et vos oreilles attentives à la prière faite en ce lieu!
“Yanzu, Allahna, bari idanunka su buɗu kunnuwanka kuma su saurara ga addu’o’in da ake miƙa a wannan wuri.
41 Maintenant, Yahweh Dieu, levez-vous, venez à votre lieu de repos, vous et l’arche de votre force! Que vos prêtres, Yahweh Dieu, soient revêtus de salut, et que vos saints jouissent du bonheur!
“Yanzu ka tashi, ya Ubangiji Allah, ka zo wurin hutunka,
42 Yahweh Dieu, ne repoussez pas la face de votre oint; souvenez-vous des grâces accordées à David, votre serviteur. »
Ya Ubangiji Allah, kada ka ƙyale shafaffenka.

< 2 Chroniques 6 >