< 2 Chroniques 30 >

1 Ezéchias envoya des messagers dans tout Israël et Juda, et il écrivit des lettres à Ephraïm et à Manassé, les invitant à venir à la maison de Yahweh à Jérusalem, pour célébrer la Pâque en l’honneur de Yahweh, le Dieu d’Israël.
Sai Hezekiya ya aika wa dukan Isra’ila da Yahuda, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa Efraim da Manasse, yana gayyatarsu su zo haikalin Ubangiji a Urushalima, su kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
2 Le roi, ses chefs et toute l’assemblée de Jérusalem, avaient tenu conseil, afin que la Pâque fut célébrée au second mois;
Sarki da fadawansa da dukan taro a Urushalima suka yanke shawara su yi Bikin Ƙetarewa a wata na biyu.
3 car on n’avait pu la faire en son temps, parce que les prêtres ne s’étaient pas sanctifiés en assez grand nombre, et que le peuple ne s’était pas rassemblé à Jérusalem.
Ba su iya yinsa a daidai lokacinsa ba domin babu isashen firistocin da suka tsarkake kansu, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba.
4 La chose parut juste aux yeux du roi et de toute l’assemblée.
Shirin ya yi kyau ga sarki da kuma dukan taron.
5 Ils décidèrent de faire passer une proclamation dans tout Israël, depuis Bersabée jusqu’à Dan, pour que l’on vint à Jérusalem célébrer la Pâque en l’honneur de Yahweh, le Dieu d’Israël; car ils ne l’avaient plus célébrée en grand nombre, selon qu’il est écrit.
Suka yanke shawara su yi shelar a ko’ina a Isra’ila, daga Beyersheba zuwa Dan, suna kiran mutane su zo Urushalima, suka kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a yi bikin da mutane masu yawa bisa ga abin da aka rubuta ba.
6 Les coureurs allèrent avec les lettres du roi et de ses chefs dans tout Israël et Juda, pour dire d’après l’ordre du roi: « Enfants d’Israël, revenez à Yahweh, le Dieu d’Abraham, d’Isaac et d’Israël, et il reviendra à ceux qui restent, à ceux d’entre vous qui ont échappé à la main des rois d’Assyrie.
Bisa ga umarnin sarki, sai’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
7 Ne soyez pas comme vos pères et comme vos frères, qui ont péché contre Yahweh, le Dieu de leurs pères, et qu’il a livrés à la désolation, comme vous le voyez.
Kada ku zama kamar iyayenku da’yan’uwanku, waɗanda suka yi rashin aminci ga Ubangiji Allah na kakanninsu, har ya mai da su abin tsoro, yadda kuke gani.
8 Ne roidissez donc pas votre cou, comme l’ont fait vos pères; donnez la main à Yahweh, venez à son sanctuaire, qu’il a sanctifié pour toujours, et servez Yahweh, votre Dieu, afin que le feu de sa colère se détourne de vous.
Kada ku yi taurinkai, yadda iyayenku suka yi; ku miƙa kai ga Ubangiji. Ku zo wuri mai tsarki, wanda ya tsarkake har abada. Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin fushi mai zafi yă juye daga gare ku.
9 Car si vous revenez à Yahweh, vos frères et vos fils trouveront miséricorde auprès de ceux qui les ont emmenés captifs, et il ne détournera pas sa face de vous, si vous revenez à lui. »
In kuka dawo wurin Ubangiji, sa’an nan waɗanda suka kama’yan’uwanku da’ya’yanku za su nuna musu tausayi, su kuma dawo wannan ƙasa, gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne mai jinƙai kuma. Ba zai kau da fuskarsa daga gare ku ba, in kuka dawo gare shi.”
10 Les coureurs passèrent ainsi de ville en ville dans le pays d’Ephraïm et de Manassé, et jusqu’à Zabulon; mais on se riait d’eux et on se moquait d’eux.
’Yan aika suka tafi gari-gari a cikin Efraim da Manasse, har zuwa Zebulun, amma mutane suka yi musu dariyar reni, suka kuma yi musu ba’a.
11 Quelques hommes seulement d’Aser, de Manassé et de Zabulon s’humilièrent et vinrent à Jérusalem.
Duk da haka, waɗansu mutanen Asher, Manasse da Zebulun suka ƙasƙantar da kansu suka tafi Urushalima.
12 Dans Juda aussi, la main de Dieu s’étendit pour leur donner un même cœur et leur faire exécuter l’ordre du roi et des chefs, selon la parole de Yahweh.
Haka ma a Yahuda, hannun Allah yana a kan mutane don yă ba su zuciya ɗaya su yi abin da sarki da fadawansa suka umarta, suna bin maganar Ubangiji.
13 Un peuple nombreux se réunit à Jérusalem pour célébrer la fête des Azymes au second mois: ce fut une immense assemblée.
Taron mutane mai girma ya haɗu a Urushalima don Bikin Burodi Marar Yisti a wata na biyu.
14 S’étant levés, ils firent disparaître les autels qui étaient à Jérusalem; ils firent aussi disparaître tous les autels des parfums, et ils les jetèrent dans la vallée du Cédron.
Suka kawar da bagadai a Urushalima suka fid da bagadan turare suka zubar da su a Kwarin Kidron.
15 Ils immolèrent ensuite la Pâque, le quatorzième jour du second mois. Les prêtres et les lévites, pris de confusion, se sanctifièrent, et offrirent des holocaustes dans la maison de Yahweh.
Suka yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu na wata na biyu. Firistoci da Lawiyawa suka ji kunya suka tsarkake kansu, suka kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
16 Ils occupaient leur place ordinaire, selon leur règlement, selon la loi de Moïse, l’homme de Dieu; et les prêtres répandaient le sang qu’ils recevaient de la main des lévites.
Sa’an nan suka ɗauki matsayinsu na kullum yadda yake a Dokar Musa mutumin Allah. Firistoci suka yayyafa jinin da Lawiyawa suka ba su.
17 Comme il y avait dans l’assemblée une foule de gens qui ne s’étaient pas sanctifiés, les lévites étaient chargés d’immoler les victimes pascales pour tous ceux qui n’étaient pas purs, afin de les consacrer à Yahweh.
Da yake da yawa cikin taron ba su tsarkake kansu ba, dole Lawiyawa su yanka’yan ragunan Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda ba su da tsarki, ba su kuma iya tsarkake ragunansu ga Ubangiji ba.
18 Car une grande partie du peuple, une foule de ceux d’Ephraïm, de Manassé, d’Issachar et de Zabulon ne s’étaient pas purifiés, et ils mangèrent la Pâque sans se conformer à ce qui est écrit. Mais Ezéchias pria pour eux, en disant: « Que Yahweh, qui est bon, pardonne
Ko da yake yawancin mutanen da suka zo daga Efraim, Manasse, Issakar da Zebulun ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci Bikin Ƙetarewa, ba tare da bin abin da yake a rubuce ba. Amma Hezekiya ya yi addu’a dominsu cewa, “Bari Ubangiji, wanda yake nagari, yă gafarta wa kowa
19 à tous ceux qui ont appliqué leur cœur à chercher Dieu, Yahweh, le Dieu de leurs pères, quoiqu’ils n’aient pas la pureté requise au sanctuaire! »
wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko da shi marar tsarki ne bisa ga dokokin wuri mai tsarki.”
20 Yahweh exauça Ezéchias et pardonna au peuple.
Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya ya kuma warkar da mutane.
21 Et les enfants d’Israël qui se trouvèrent à Jérusalem célébrèrent la fête des Azymes pendant sept jours avec une grande joie, et chaque jour les lévites et les prêtres louaient Yahweh avec les instruments puissants, en l’honneur de Yahweh.
Isra’ilawan da suka kasance a Urushalima suka yi Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai da farin ciki mai girma, yayinda Lawiyawa da firistoci suke rera ga Ubangiji kowace rana, haɗe da kayan kiɗin yabon Ubangiji.
22 Ezéchias parla au cœur de tous les lévites, qui montraient une grande intelligence pour le service de Yahweh. Ils mangèrent les victimes de la fête pendant sept jours, offrant des sacrifices pacifiques et louant Yahweh, le Dieu de leurs pères.
Hezekiya ya yi magana mai ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna ganewar fasaha a hidimar Ubangiji. Kwana bakwai suka ci rabonsu da aka tsara, suka miƙa hadayun salama, suka kuma yabi Ubangiji Allah na kakanninsu.
23 Toute l’assemblée fut d’avis de célébrer sept autres jours, et ils célébrèrent sept autres jours joyeusement;
Dukan mutanen suka yarda su ƙara kwana bakwai kuma, sai suka ci gaba da bikin cikin farin ciki har waɗansu kwana bakwai kuma.
24 car Ezéchias, roi de Juda, avait donné à l’assemblée mille taureaux et sept mille brebis, et les chefs lui avaient donné mille taureaux et dix mille brebis, et des prêtres en grand nombre s’étaient sanctifiés.
Hezekiya sarkin Yahuda ya tanada bijimai dubu ɗaya da tumaki da kuma awaki dubu bakwai wa taron, fadawa kuma suka tanada musu bijimai dubu da kuma tumaki da awaki dubu goma. Firistoci masu yawa suka tsarkake kansu.
25 Toute l’assemblée de Juda, les prêtres et les lévites, toute l’assemblée venue d’Israël et les étrangers venus du pays d’Israël ou établis en Juda se livrèrent à la joie.
Taron gaba ɗaya na Yahuda suka yi farin ciki, tare da firistoci da kuma Lawiyawa da dukan waɗanda suka taru daga Isra’ila, har ma da baƙi waɗanda suka zo daga Isra’ila da waɗanda suke zama a Yahuda.
26 Il y eut à Jérusalem de grandes réjouissances, au point que depuis le temps de Salomon, fils de David, roi d’Israël, rien de semblable n’avait eu lieu dans Jérusalem.
Aka yi farin ciki mai girma a Urushalima, gama tun zamanin Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila, ba a taɓa yin wani abu kamar haka a Urushalima ba.
27 Les prêtres lévitiques se levèrent et bénirent le peuple, et leur voix fut entendue; leur prière arriva jusqu’à la sainte demeure de Yahweh, jusqu’au ciel.
Firistoci da Lawiyawa suka tsaya suka albarkace mutane, Allah kuma ya ji su, gama addu’arsu ya kai sama, mazauninsa mai tsarki.

< 2 Chroniques 30 >