< 2 Chroniques 28 >

1 Achaz avait vingt ans lorsqu’il devint roi, et il régna seize ans à Jérusalem. Il ne fit pas ce qui est droit aux yeux de Yahweh, comme avait fait David, son père.
Ahaz yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Ba kamar Dawuda kakansa ba, bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ba.
2 Il marcha dans les voies des rois d’Israël, et même il fit des images en fonte pour les Baals.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila ya kuma yi zubin gumaka domin a bauta wa Ba’al.
3 Il brûla des parfums dans la vallée de Ben-Hinnom, et il fit passer ses fils par le feu, selon les abominations des nations que Yahweh avait chassées devant les enfants d’Israël.
Ya ƙone hadayu a Kwarin Ben Hinnom, ya kuma miƙa’ya’yansa maza a cikin wuta, yana bin hanyoyi banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 Il offrait des sacrifices et des parfums aux hauts lieux, sur les collines et sous tout arbre vert.
Ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a masujadan kan tudu, a bisa tuddai da kuma ƙarƙashin kowane itace mai inuwa.
5 Yahweh, son Dieu, le livra entre les mains du roi de Syrie; les Syriens le battirent et lui firent un grand nombre de prisonniers, qu’ils emmenèrent à Damas. Il fut aussi livré entre les mains du roi d’Israël, qui le frappa d’une grande défaite.
Saboda haka Ubangiji Allahnsa ya miƙa shi ga sarkin Aram. Arameyawa suka ci shi a yaƙi, suka kuma kwashe mutanensa da yawa a matsayin’yan kurkuku, suka kawo Damaskus. Ya kuma ba da shi ga sarkin Isra’ila, wanda ya jijji masa a yaƙi.
6 Phacée, fils de Romélias, tua en Juda dans un seul jour cent vingt mille hommes, tous vaillants, parce qu’ils avaient abandonné Yahweh, le Dieu de leurs pères.
A rana ɗaya Feka ɗan Remaliya ya kashe sojoji dubu ɗari da dubu ashirin a Yahuda, domin Yahuda sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu.
7 Zéchri, guerrier d’Ephraïm, tua Maasias, fils du roi, et Ezrica, chef de la maison royale, et Elcana, le second après le roi.
Zikri, wani jarumin Efraim, ya kashe Ma’asehiya ɗan sarki, Azrikam hafsa mai lura da fada, da kuma Elkana, mataimakin sarki.
8 Les enfants d’Israël firent parmi leurs frères deux cent mille prisonniers, femmes, fils et filles, et ils leur prirent un butin considérable et ils emmenèrent le butin à Samarie.
Isra’ilawa suka kame kamammu daga’yan’uwansu mata,’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata dubu ɗari biyu. Suka kuma kwashe ganima mai yawan gaske, waɗanda suka kwasa zuwa Samariya.
9 Il y avait là un prophète de Yahweh, nommé Oded. Sortant au-devant de l’armée qui revenait à Samarie, il leur dit: « Voici que, dans sa colère contre, Juda, Yahweh, le Dieu de vos pères, les a livrés entre vos mains; et vous les avez tués avec une fureur qui a atteint jusqu’au ciel.
Amma wani annabin Ubangiji mai suna Oded yana a can, sai ya fito don yă sadu da mayaƙa sa’ad da suke komowa zuwa Samariya. Ya ce musu, “Domin Ubangiji Allah na kakanninku yana fushi da Yahuda, ya ba da su cikin hannunku. Sai kuka kashe su cikin fushin da ya kai sama.
10 Et maintenant, vous songez à soumettre les enfants de Juda et de Jérusalem pour qu’ils soient vos serviteurs et vos servantes! Mais vous, n’avez-vous pas aussi des offenses à l’égard de Yahweh, votre Dieu?
Yanzu kuma kuna niyya ku mai da maza da matan Yahuda da Urushalima bayinku. Amma ku ɗin ba ku da laifin zunubi ga Ubangiji Allahnku ne?
11 Et maintenant, écoutez-moi, et renvoyez ces captifs que vous avez faits parmi vos frères, car l’ardeur de la colère de Yahweh est sur vous. »
To, ku saurare ni! Ku mai da’yan’uwanku da kuka kama a matsayin’yan kurkuku, gama fushin Ubangiji yana a kanku.”
12 Quelques-uns d’entre les chefs des enfants d’Ephraïm, Azarias, fils de Johanan, Barachias, fils de Mosollamoth, Ezéchias, fils de Sellum, et Amasa, fils d’Adali, s’élevèrent contre ceux qui revenaient de l’armée,
Sai waɗansu shugabanni a Efraim, Azariya ɗan Yehohanan, Berekiya ɗan Meshillemot, Hezekiya ɗan Shallum da Amasa ɗan Hadlai, suka tasar wa waɗanda suke isowa daga yaƙi.
13 et leur dirent: « Vous ne ferez pas entrer ici les captifs; car c’est pour nous charger d’une faute envers Yahweh que vous songez à ajouter à nos péchés et à nos fautes; car grande est notre faute, et l’ardeur de la colère de Yahweh est sur Israël. »
Suka ce, “Dole ku kawo waɗannan’yan kurkukun a nan, ko kuwa za ku yi laifi a gaban Ubangiji. Kuna niyya ku ƙara ga zunubinmu da kuma laifinmu? Gama laifinmu ya riga ya yi yawa, kuma fushinsa mai tsanani yana a kan Isra’ila.”
14 Les soldats abandonnèrent les captifs et le butin devant les chefs et devant toute l’assemblée.
Saboda haka sojoji suka ba da’yan kurkukun da ganima a gaban hafsoshi da dukan taron.
15 Et les hommes qui ont été mentionnés par leurs noms se levèrent et, ayant pris les captifs, ils revêtirent avec le butin tous ceux qui étaient nus, leur donnant des habits et des chaussures; puis ils les firent manger et boire et les oignirent et, transportant sur des ânes tous ceux qui défaillaient, il les menèrent à Jéricho, la ville des palmiers, auprès de leurs frères. Et eux retournèrent à Samarie.
Sai mutanen da aka kira sunansu suka tashi, suka ɗauki kamammun, da ganimar, suka sa wa dukan waɗanda suke tsirara sutura. Suka sa musu sutura, suka ba su takalma, suka ba su abinci da abin sha, suka shafa musu mai. Suka hawar da dukan raunana a kan jakuna, suka kai su wurin’yan’uwansu a Yeriko, wato, Birnin Itatuwan Dabino, sa’an nan suka koma Samariya.
16 En ce temps-là, le roi Achaz envoya demander aux rois d’Assyrie de le secourir.
A lokacin nan Sarki Ahaz ya aika wurin sarkin Assuriya neman taimako.
17 Car les Edomites étaient encore venus; ils avaient battu Juda et emmené des captifs.
Mutanen Edom sun sāke zuwa suka yaƙi Yahuda suka kuma kwashe’yan kurkuku,
18 Les Philistins s’étaient répandus dans les villes de la Séphéla et du Négeb de Juda; ils avaient pris Bethsamès, Aïalon, Gadéroth, Socho et les villes de sa dépendance, Thamna et les villes de sa dépendance, Gamzo et les villes de sa dépendance, et s’y étaient établis.
yayinda Filistiyawa suka kai hari wa garuruwa a gindin tuddai da kuma a Negeb na Yahuda. Suka kame su suka kuma zauna a Bet-Shemesh, Aiyalon da Gederot, haka ma Soko, Timna da Gimzo tare da ƙauyuka kewayensu.
19 Car Yahweh humiliait Juda, à cause d’Achaz, roi d’Israël, qui avait déchaîné la licence dans Juda et commis des fautes contre Yahweh.
Ubangiji ya ƙasƙantar da Yahuda saboda Ahaz sarkin Isra’ila, gama ya hadasa mugunta a Yahuda kuma ya kasance marar aminci ga Ubangiji.
20 Thelgath-Phalnasar, roi d’Assyrie, vint contre lui, le traita avec rigueur et ne le fortifia pas.
Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo wurinsa, sai ya wahalar da sarki Ahaz maimakon taimakonsa.
21 Car Achaz avait dépouillé la maison de Yahweh, la maison du roi et des chefs, et fait des présents au roi d’Assyrie: ce qui ne lui fut d’aucun secours.
Ahaz ya ɗauki waɗansu abubuwa daga haikalin Ubangiji da kuma daga fadan sarki da kuma daga sarakuna, ya ba da su ga sarkin Assuriya, amma wannan bai taimake shi ba.
22 Pendant qu’il était dans la détresse, il continuait à offenser Yahweh, lui, le roi Achaz.
Cikin lokacin wahalarsa Sarki Ahaz ya ƙara zama marar aminci ga Ubangiji.
23 Il sacrifia aux dieux de Damas, qui le frappaient, et il dit: « Puisque les dieux des rois de Syrie leur viennent en aide, je leur offrirai des sacrifices et ils me secourront. » Mais ils furent une cause de chute pour lui et pour tout Israël.
Ya miƙa hadayu ga allolin Damaskus, waɗanda suka ci shi a yaƙi; gama ya yi tunani, “Da yake allolin sarakunan Aram sun taimake su, zan miƙa hadayu domin su taimake ni.” Amma suka zama sanadin fāɗuwarsa da kuma fāɗuwar dukan Isra’ila.
24 Achaz rassembla les ustensiles de la maison de Dieu et mit en pièces les ustensiles de la maison de Dieu, et, ayant fermé les portes de la maison de Yahweh, il se fit des autels à tous les angles de Jérusalem.
Ahaz ya tattara kayayyaki daga haikalin Allah ya kwashe su. Ya kulle ƙofofin haikalin Ubangiji ya kakkafa bagadai a kowace kusurwa a titin Urushalima.
25 Il établit des hauts lieux dans chacune des villes de Juda pour offrir des parfums à d’autres dieux. Il irrita ainsi Yahweh, le Dieu de ses pères.
A kowane gari a Yahuda, ya gina masujadan kan tudu don ƙone hadayu ga waɗansu alloli, ya kuma tsokane Ubangiji Allah na kakanninsa ya yi fushi.
26 Le reste de ses actes et toutes ses voies, les premières et les dernières, voici que cela est écrit dans le livre des rois de Juda et d’Israël.
Sauran ayyukan mulkinsa da dukan hanyoyinsa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Achaz se coucha avec ses pères, et on l’enterra dans la ville, dans Jérusalem, car on ne l’introduisit pas dans les sépulcres des rois d’Israël. Ezéchias, son fils, régna à sa place.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Urushalima, amma ba a sa shi a makabartan sarakunan Isra’ila ba. Sai Hezekiya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Chroniques 28 >