< 2 Chroniques 21 >

1 Josaphat se coucha avec ses pères, et il fut enterré avec ses pères dans la ville de David; Joram, son fils, régna à sa place.
Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 Joram avait des frères, fils de Josaphat: Azarias, Jahiel, Zacharias, Azarias, Michaël et Saphatias; ils étaient tous fils de Josaphat, roi de Juda.
’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
3 Leur père leur avait donné des présents considérables en or et en argent, et en objets de prix, avec des villes fortes en Juda; mais il laissa le royaume à Joram, parce qu’il était le premier-né.
Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
4 Joram s’établit sur le royaume de son père et, lorsqu’il se fut affermi, il fit mourir par l’épée tous ses frères, et aussi quelques-uns des chefs d’Israël.
Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
5 Joram avait trente-deux ans lorsqu’il devint roi, et il régna huit ans à Jérusalem.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
6 Il marcha dans la voie des rois d’Israël, comme avait fait la maison d’Achab, car il avait pour femme une fille d’Achab, et il fit ce qui est mal aux yeux de Yahweh.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
7 Mais Yahweh ne voulut pas détruire la maison de David, à cause de l’alliance qu’il avait contractée avec David, et parce qu’il lui avait dit qu’il lui donnerait toujours une lampe, à lui et à ses fils.
Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
8 De son temps, Edom se révolta contre la domination de Juda et se donna un roi.
A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
9 Joram se mit en marche avec ses chefs et tous ses chars; s’étant levé de nuit, il battit les Edomites qui l’entouraient et les chefs des chars.
Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
10 Edom s’affranchit de la domination de Juda, jusqu’à ce jour. Lobna s’affranchit aussi dans le même temps de sa domination, parce qu’il avait abandonné Yahweh, le Dieu de ses pères.
Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
11 Joram fit même des hauts lieux dans les montagnes de Juda; il poussa à la prostitution les habitants de Jérusalem, et il séduisit Juda.
Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
12 Il lui vint un écrit de la part du prophète Elie, disant: « Ainsi dit Yahweh, le Dieu de David, ton père: Parce que tu n’as pas marché dans les voies de Josaphat, ton père, et dans les voies d’Asa, roi de Juda,
Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
13 mais que tu as marché dans la voie des rois d’Israël; parce que tu as poussé à la prostitution Juda et les habitants de Jérusalem, comme la maison d’Achab poussait Israël à la prostitution, et parce que tu as fait mourir tes frères, meilleurs que toi, la maison même de ton père:
Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
14 voici que Yahweh frappera d’une grande plaie ton peuple, tes fils, tes femmes et tout ce qui t’appartient;
Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
15 et toi, tu seras frappé de graves maladies, d’une maladie d’entrailles, telle que tes entrailles sortiront par la violence du mal, pendant de nombreux jours ».
Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
16 Et Yahweh excita contre Joram l’esprit des Philistins et des Arabes voisins des Ethiopiens.
Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
17 Etant montés en Juda, ils s’y répandirent, pillèrent toutes les richesses qui se trouvaient dans la maison du roi, et emmenèrent aussi ses fils et ses femmes, de sorte qu’il ne lui resta plus d’autre fils que Joachaz, le plus jeune de ses fils.
Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
18 Après tout cela, Yahweh le frappa dans ses entrailles d’une maladie sans remède.
Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
19 Les jours s’écoulant, sur la fin de la seconde année, les entrailles de Joram sortirent par la violence de son mal. Il mourut dans de grandes souffrances, et son peuple ne brûla pas de parfums en son honneur, comme il en avait brûlé pour ses pères.
Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
20 Joram avait trente-deux ans lorsqu’il devint roi, et il régna huit ans à Jérusalem. Il s’en alla sans être regretté, et on l’enterra dans la ville de David, mais non dans les sépulcres des rois.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.

< 2 Chroniques 21 >