< 2 Chroniques 16 >

1 La trente-sixième année du règne d’Asa, Baasa, roi d’Israël, monta contre Juda, et il bâtit Rama, pour empêcher les gens d’Asa, roi de Juda, de sortir et d’entrer.
A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura don yă yaƙi Yahuda da Rama mai katanga, don kuma yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa sarkin Yahuda.
2 Asa tira de l’argent et de l’or des trésors de la maison de Yahweh et de la maison du roi, et il envoya des messagers à Ben-Hadad, roi de Syrie, qui habitait à Damas, pour dire:
Sai Asa ya ɗauki azurfa da zinariya daga ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma na fadansa ya aika wa Ben-Hadad sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
3 « Qu’il y ait une alliance entre moi et toi, comme il y en avait une entre mon père et ton père. Je t’envoie de l’argent et de l’or. Va, romps ton alliance avec Baasa, roi d’Israël, afin qu’il s’éloigne de moi. »
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakani na da kai kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Dubi ina aika maka azurfa da zinariya. Yanzu ka yanke yarjejjeniya da Ba’asha sarkin Isra’ila domin yă janye daga gare ni.”
4 Ben-Hadad écouta le roi Asa; il envoya les chefs de son armée contre les villes d’Israël, et ils battirent Ahion, Dan, Abel-Maïm et toutes les villes à magasins de Nephthali.
Ben-Hadad ya yarda da Sarki Asa ya kuma aika da manyan hafsoshin mayaƙansa a kan garuruwan Isra’ila. Suka ci Iyon, Dan, Abel-Mayim da kuma dukan biranen ajiya na Naftali.
5 Baasa, l’ayant appris, cessa de bâtir Rama, et interrompit ses travaux.
Da Ba’asha ya ji wannan, ya daina ginin Rama ya yashe aikinsa.
6 Le roi Asa prit tout Juda, et ils emportèrent les pierres et le bois avec lesquels Baasa construisait Rama; et il bâtit avec elles Gabaa et Maspha.
Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
7 En ce temps-là, Hanani le voyant vint auprès d’Asa, roi de Juda, et lui dit: « Parce que tu t’es appuyé sur le roi de Syrie et que tu ne t’es pas appuyé sur Yahweh, ton Dieu, à cause de cela, l’armée du roi de Syrie s’est échappée de tes mains.
A lokacin Hanani mai duba ya zo wurin Asa sarkin Yahuda ya ce masa, “Don ka dogara ga sarkin Aram, ba kuwa ga Ubangiji Allahnka ba ne mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.
8 Les Ethiopiens et les Lybiens ne formaient-ils pas une grande armée, avec des chars, et des cavaliers très nombreux? Et cependant, parce que tu t’étais appuyé sur Yahweh, il les a livrés entre tes mains.
Ai, Kushawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da kekunan yaƙi da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, ya kuwa ba da su cikin hannunka.
9 Car les yeux de Yahweh parcourent toute la terre pour soutenir ceux dont le cœur est parfaitement à lui. Tu as donc agi en insensé dans cette affaire, car désormais tu auras des guerres. »
Gama gaban Ubangiji yana ko’ina a duniya don yă ƙarfafa waɗanda zukatansu suke binsa cikin aminci. Ka yi wauta, daga yanzu nan gaba za ka yi ta yaƙi.”
10 Asa fut irrité contre le voyant, et il le fit mettre en prison, car il était en colère contre lui à cause de ses paroles. Dans le même temps, Asa opprima quelques-uns du peuple.
Sai Asa ya yi fushi sosai da mai duban saboda wannan; ya yi fushi ƙwarai har ya sa aka jefa shi a kurkuku. A lokaci guda kuma Asa ya fara gwada wa mutane azaba.
11 Et voici que les actes d’Asa, les premiers et les derniers, sont écrits dans le livre des rois de Juda et d’Israël.
Ayyukan mulkin Asa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
12 Dans la trente-neuvième année de son règne, Asa eut les pieds malades au point d’éprouver de grandes souffrances; mais, même pendant sa maladie, il ne chercha pas Yahweh, mais les médecins.
A shekara ta talatin da tara ta mulkinsa, Asa ya kamu da wata cuta a ƙafarsa. Ko da yake cutar ta yi tsanani, duk d haka ma a cikin ciwonsa bai nemi taimako daga Ubangiji ba, sai dai daga likitoci.
13 Asa se coucha avec ses pères, et il mourut la quarante-unième année de son règne.
Sa’an nan a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa, Asa ya mutu ya kuma huta tare da kakanninsa.
14 On l’enterra dans son sépulcre qu’il s’était creusé dans la ville de David; on le coucha sur un lit qu’on avait rempli de parfums et d’aromates préparés selon l’art du parfumeur, et l’on en brûla une quantité très considérable.
Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.

< 2 Chroniques 16 >