< 1 Samuel 24 >

1 Lorsque Saül fut revenu de la poursuite des Philistins, on vint lui dire: « Voici que David est au désert d’Engaddi. »
Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
2 Saül prit trois mille hommes d’élite d’entre tout Israël, et il alla à la recherche de David et de ses gens jusque sur les rochers des boucs sauvages.
Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
3 Il arriva aux parcs des brebis qui étaient près du chemin; il y avait là une caverne, où Saül entra pour se couvrir les pieds; et David et ses gens étaient assis au fond de la caverne.
Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
4 Les hommes de David lui dirent: « Voici le jour dont Yahweh t’a dit: Voici que je livre ton ennemi entre tes mains; traite-le comme il te plaira. » David se leva et coupa à la dérobée le pan du manteau de Saül.
Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
5 Après cela, le cœur de David lui battit, de ce qu’il avait coupé le pan du manteau de Saül.
Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
6 Et il dit à ses hommes: « Que Yahweh me préserve de faire contre mon seigneur, l’oint de Yahweh, une chose telle que de porter ma main sur lui, car il est l’oint de Yahweh! »
Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
7 Par ses paroles, David réprima ses hommes et ne leur permit pas de se jeter sur Saül. Saül s’étant levé pour sortir de la caverne continua sa route.
Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
8 Après cela David se leva et, sortant de la caverne, il se mit à crier après Saül en disant: « O roi, mon seigneur! » Saül regarda derrière lui, et David s’inclina le visage contre terre et se prosterna.
Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
9 Et David dit à Saül: « Pourquoi écoutes-tu les propos de gens qui disent: Voici que David cherche à te faire du mal?
Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
10 Voici qu’aujourd’hui tes yeux ont vu comment Yahweh t’a livré, aujourd’hui même, entre mes mains dans la caverne. On me disait de te tuer; mais mon œil a eu pitié de toi, et j’ai dit: Je ne porterai pas ma main sur mon seigneur, car il est l’oint de Yahweh.
Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
11 Vois donc, mon père, vois dans ma main le pan de ton manteau. Puisque j’ai coupé le pan de ton manteau et que je ne t’ai pas tué, reconnais et vois qu’il n’y a dans ma conduite ni méchanceté ni révolte, et que je n’ai pas péché contre toi. Et toi, tu fais la chasse à ma vie pour me l’ôter.
Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
12 Que Yahweh soit juge entre moi et toi, et que Yahweh me venge de toi! Mais ma main ne sera pas sur toi.
Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
13 Des méchants vient la méchanceté, dit le vieux proverbe; aussi ma main ne sera pas sur toi.
Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
14 Après qui le roi d’Israël s’est-il mis en marche? Qui poursuis-tu? Un chien mort? Une puce?
“Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
15 Que Yahweh juge et prononce entre toi et moi. Qu’il regarde et qu’il défende ma cause, et que sa sentence me délivre de ta main! »
Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
16 Lorsque David eut achevé d’adresser ces paroles à Saül, Saül dit: « Est-ce bien ta voix, mon fils David? » Et Saül éleva la voix et pleura.
Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
17 Il dit à David: « Tu es plus juste que moi; car toi tu m’as fait du bien, et moi je t’ai rendu du mal.
Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
18 Tu as montré aujourd’hui que tu agis avec bonté envers moi, puisque Yahweh m’a livré entre tes mains et que tu ne m’as pas tué.
Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
19 Si quelqu’un rencontre son ennemi, le laisse-t-il poursuivre en paix son chemin? Que Yahweh te fasse du bien en retour de ce que tu m’as fait en ce jour!
In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
20 Maintenant, voici que je sais que tu seras roi et que la royauté d’Israël sera stable entre tes mains.
Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
21 Jure-moi donc par Yahweh que tu ne détruiras pas ma postérité après moi, et que tu ne retrancheras pas mon nom de la maison de mon père. »
Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
22 David le jura à Saül. Et Saül s’en alla dans sa maison, et David et ses hommes montèrent à l’endroit fort.
Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.

< 1 Samuel 24 >