< 1 Rois 21 >

1 Après ces événements, comme Naboth de Jezrahel avait une vigne à Jezrahel, à côté du palais d’Achab, roi de Samarie,
Ana nan bayan haka sai waɗannan abubuwa suka faru. Nabot mutumin Yezireyel yana da gonar inabi a Yezireyel, a yankin Samariya, kusa da gidan Sarki Ahab.
2 Achab parla à Naboth en ces termes: « Cède-moi ta vigne pour qu’elle me serve de jardin potager, car elle est tout près de ma maison; je te donnerai à la place une vigne meilleure, ou, si cela te convient, de l’argent pour sa valeur. »
Sai Ahab ya ce wa Nabot, “Ka ba ni gonar inabinka in yi amfani da ita don kayan lambu, da yake tana kusa da fadana. Zan ba ka wata gonar inabin da ta fi wannan, ko kuma in ka gwammace, sai in biya ka duk abin da ya dace da ita.”
3 Naboth répondit à Achab: « Que Yahweh me garde de te donner l’héritage de mes pères! »
Amma Nabot ya amsa wa Ahab ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe in ba ka gādon kakannina.”
4 Achab rentra dans sa maison sombre et irrité à cause de cette parole que lui avait dite Naboth de Jezrahel: « Je ne donnerai pas l’héritage de mes pères. » Et, se couchant sur son lit, il détourna le visage et ne mangea pas.
Ahab ya cika da fushi saboda Nabot, mutumin Yezireyel ya ce, “Ba zan ba ka gādon kakannina ba.” Ya kwanta a gadonsa yana zub da hawaye, ya kuma ƙi cin abinci.
5 Jézabel, sa femme, vint auprès de lui et lui dit: « Pourquoi as-tu l’âme sombre et ne manges-tu pas? »
Matarsa Yezebel ta shiga ciki ta tambaye shi, ta ce, “Me ya sa ka kumbura? Me ya sa ba za ka ci abinci ba?”
6 Il lui répondit: « J’ai parlé à Naboth de Jezrahel et je lui ai dit: Cède-moi ta vigne pour de l’argent; ou, si tu l’aimes mieux, je te donnerai une autre vigne à la place. Mais il a dit: Je ne te donnerai pas ma vigne. »
Sai ya amsa mata, ya ce, “Domin na ce wa Nabot mutumin Yezireyel, ‘Ka sayar mini gonar inabinka; ko kuwa in ka gwammace, zan ba ka wata gonar inabi a maimakonta.’ Amma ya ce, ‘Ba zan ba ka gonar inabina ba.’”
7 Alors Jézabel, sa femme, lui dit: « Est-ce toi qui exerces maintenant la royauté sur Israël? Lève-toi, prends de la nourriture, et que ton cœur se réjouisse; je te donnerai, moi, la vigne de Naboth de Jezrahel. »
Yezebel matarsa ta ce, “Yaya kake yi kamar ba kai ne sarki Isra’ila ba? Tashi ka ci abinci! Ka yi farin ciki. Zan ba ka gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel.”
8 Et elle écrivit au nom d’Achab une lettre qu’elle scella du sceau du roi, et elle envoya la lettre aux anciens et aux magistrats qui étaient dans la ville et habitaient avec Naboth.
Sai ta rubuta wasiƙu a sunan Ahab, ta buga hatiminsa a kansu, sa’an nan ta aika su ga dattawa da manyan gari waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake.
9 Voici ce qu’elle écrivit dans la lettre: « Publiez un jeûne; placez Naboth en tête du peuple,
Cikin waɗannan wasiƙu ta rubuta, “Ku yi shelar ranar azumi, ku zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
10 et mettez en face du lui deux hommes de Bélial qui déposeront contre lui en ces termes: Tu as maudit Dieu et le roi! Puis menez-le dehors, lapidez-le, et qu’il meure. »
Amma ku zaunar da waɗansu’yan iska biyu ɗaura da shi, ku sa su ba da shaida cewa ya zagi Allah da sarki. Sa’an nan ku ɗauke shi ku jajjefe shi da dutse sai ya mutu.”
11 Les gens de la ville de Naboth, les anciens et les magistrats qui habitaient dans sa ville, firent selon que leur avait envoyé dire Jézabel, selon qu’il était écrit dans la lettre qu’elle leur avait envoyée.
Sai dattawa da manyan gari, waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake, suka yi kamar yadda Yezebel ta umarta a cikin wasiƙun da ta rubuta.
12 Ils publièrent un jeûne, et ils placèrent Naboth en tête du peuple,
Suka yi shelar azumi, suka kuma zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
13 et les deux hommes, fils de Bélial, vinrent se mettre en face de lui. Ces hommes de Bélial déposèrent contre Naboth devant le peuple en ces termes: « Naboth a maudit Dieu et le roi! » Puis ils le menèrent hors de la ville et le lapidèrent, et il mourut.
Sa’an nan’yan iska biyu suka zo, suka zauna ɗaura da shi, suka kawo zarge a kan Nabot a gaban mutane, suna cewa, “Nabot ya zagi Allah da sarki.” Saboda haka aka ɗauke shi waje da birnin, aka jajjefe shi da dutse har ya mutu.
14 Et ils envoyèrent dire à Jézabel: « Naboth a été lapidé, et il est mort. »
Sa’an nan suka aika wa Yezebel. “An jajjefe Nabot, ya kuma mutu.”
15 Lorsque Jézabel eut appris que Naboth avait été lapidé et qu’il était mort, elle dit à Achab: « Lève-toi, prends possession de la vigne de Naboth de Jezrahel, qui a refusé de te la céder pour de l’argent; car Naboth n’est plus en vie, car il est mort. »
Nan da nan sa’ad da Yezebel ta ji cewa an jajjefe Nabot da dutse ya kuma mutu, sai ta ce wa Ahab, “Tashi ka mallaki gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel wanda ya ƙi ya sayar maka. Ba shi da rai, ya mutu.”
16 Lorsqu’Achab eut appris que Naboth était mort, il se leva pour descendre à la vigne de Naboth de Jezrahel, afin d’en prendre possession.
Da Ahab ya ji cewa Nabot ya mutu, sai ya tashi ya gangara don yă mallaki gonar inabin Nabot.
17 Alors la parole de Yahweh fut adressée à Elie, le Thesbite, en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe.
18 « Lève-toi, descends au devant d’Achab, roi d’Israël, qui règne à Samarie; le voilà dans la vigne de Naboth, où il est descendu pour en prendre possession.
Ta ce, “Gangara don ka sadu da Ahab sarkin Isra’ila, wanda yake mulki a Samariya. Yanzu yana a gonar inabin Nabot, inda ya tafi yă mallake ta.
19 Tu lui parleras en ces termes: Ainsi dit Yahweh: “N’as-tu pas tué et pris un héritage?” Et tu lui parleras en ces termes: “Ainsi dit Yahweh: Au lieu même où les chiens ont léché le sang de Naboth, les chiens lécheront aussi ton propre sang.” »
Ka ce masa, Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba ka kashe mutum ka kuma ƙwace kayansa ba?’ Sa’an nan ka ce masa ga abin da Ubangiji ya ce, ‘A inda karnuka suka lashe jinin Nabot, karnuka za su lashe jininka, I, naka!’”
20 Achab dit à Elie: « M’as-tu trouvé, ô mon ennemi? » Il répondit: « Je t’ai trouvé, parce que tu t’es vendu pour faire ce qui est mal aux yeux de Yahweh.
Ahab ya ce wa Iliya, “Wato, ka same ni kuma, abokin gābana!” Sai ya amsa ya ce, “Na same ka, domin ka sayar da kanka ga yin mugunta a gaban Ubangiji.
21 Voici que je ferai venir le malheur sur toi; je te balaierai; j’exterminerai tout mâle appartenant à Achab, celui qui est esclave et celui qui est libre en Israël,
‘Zan kawo masifa a kanka. Zan kawar da zuriyarka, in kuma yanke daga Ahab kowane ɗa namiji na ƙarshe cikin Isra’ila, bawa ko’yantacce.
22 et je rendrai ta maison semblable à la maison de Jéroboam, fils de Nabat, et à la maison de Baasa, fils d’Ahias, parce que tu m’as provoqué à la colère et que tu as fait pécher Israël. »
Zan mai da gidanka kamar gida Yerobowam ɗan Nebat, da na Ba’asha ɗan Ahiya, domin ka tsokane ni har na yi fushi, ka kuma sa Isra’ila ya yi zunubi.’
23 Yahweh parla aussi contre Jézabel en ces termes: « Les chiens mangeront Jézabel près du fossé de Jezrahel.
“Game da Yezebel kuwa Ubangiji ya ce, ‘Karnuka za su cinye Yezebel a katangar Yezireyel.’
24 Celui de la maison d’Achab qui mourra dans la ville sera mangé par les chiens, et celui qui mourra dans les champs sera mangé par les oiseaux du ciel. »
“Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ahab waɗanda suka mutu a cikin birni, tsuntsayen sararin sama kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
25 Il n’y a eu vraiment personne qui se soit vendu comme Achab pour faire ce qui est mal aux yeux de Yahweh; parce que Jézabel, sa femme, l’excitait.
(Babu wani mutum kamar Ahab, wanda ya ba da kansa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji. Yezebel matarsa ce ta zuga shi.
26 Il s’est conduit de la manière la plus abominable, en allant après les idoles, selon tout ce que faisaient les Amorrhéens que Yahweh chassa devant les enfants d’Israël.
Ya yi abar ƙyama ƙwarai ta wurin bin gumaka, kamar Amoriyawan da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ila.)
27 Lorsqu’Achab eut entendu les paroles d’Elie, il déchira ses vêtements et, ayant mis un sac sur son corps, il jeûna; il couchait avec le sac et il marchait avec lenteur.
Sa’ad da Ahab ya ji waɗannan kalmomi, sai ya yage rigarsa, ya sa rigunan makoki, ya kuma yi azumi. Ya kwanta a kayan makoki, ya kuma yi tafiya cikin sauƙinkai.
28 Et la parole de Yahweh fut adressée à Elie le Thesbite, en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe, ta ce,
29 « As-tu vu comment Achab s’est humilié devant moi? Parce qu’il s’est humilié devant moi, je ne ferai pas venir le malheur pendant sa vie; ce sera pendant la vie de son fils que je ferai venir le malheur sur sa maison. »
“Ka lura da yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa a gabana kuwa? Domin ya ƙasƙantar da kansa, ba zan kawo wannan masifa a kwanakinsa ba, amma zan kawo ta a kan gidansa a kwanakin ɗansa.”

< 1 Rois 21 >