< 1 Rois 14 >

1 Dans ce temps-là, Abia, fils de Jéroboam, était devenu malade.
A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
2 Jéroboam dit à sa femme: « Lève-toi, je te prie, et déguise-toi pour qu’on ne sache pas que tu es la femme de Jéroboam, et va à Silo. Voici que là se trouve Ahias, le prophète, celui qui m’a dit que je serais roi sur ce peuple.
sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
3 Prends avec toi dix pains, des gâteaux et un vase de miel, et entre chez lui: il te dira ce qui doit arriver à l’enfant. »
Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
4 La femme de Jéroboam fit ainsi; s’étant levée, elle alla à Silo et entra dans la maison d’Ahias. Or Ahias ne pouvait plus voir, parce que la vieillesse avait obscurci ses yeux.
Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
5 Yahweh avait dit à Ahias: « Voici que la femme de Jéroboam vient pour obtenir de toi une parole au sujet de son fils, qui est malade; tu lui parleras de telle et telle manière. Quand elle arrivera, elle se donnera pour une autre. »
Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
6 Quand Ahias entendit le bruit de ses pas, au moment où elle franchissait la porte, il dit: « Entre, femme de Jéroboam; pourquoi te donnes-tu pour une autre? Je suis chargé pour toi d’un dur message.
Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
7 Va, dis à Jéroboam: Ainsi parle Yahweh, Dieu d’Israël: Je t’ai élevé du milieu du peuple et je t’ai établi chef sur mon peuple d’Israël;
Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
8 j’ai arraché le royaume de la maison de David, et je te l’ai donné; mais tu n’as pas été comme mon serviteur David, qui a observé mes commandements et marché après moi de tout son cœur, ne faisant que ce qui est droit à mes yeux;
Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
9 mais tu as fait le mal plus que tous ceux qui ont été avant toi, tu es allé te faire d’autres dieux et des images de fonte pour m’irriter, et tu m’as rejeté derrière ton dos!
Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
10 C’est pourquoi voici que je vais faire venir le malheur sur la maison de Jéroboam; j’exterminerai tout mâle appartenant à Jéroboam, celui qui est esclave et celui qui est libre et Israël, et je balaierai la maison de Jéroboam, comme on balaie l’ordure, jusqu’à ce qu’il n’en reste plus.
“‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
11 Celui de la maison de Jéroboam qui mourra dans la ville sera mangé par les chiens, et celui qui mourra dans les champs sera mangé par les oiseaux du ciel: car Yahweh a parlé.
Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
12 Et toi, lève-toi, va dans ta maison; dès que tes pieds entreront dans la ville, l’enfant mourra.
“Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
13 Tout Israël le pleurera, et on l’enterrera car il est le seul de la maison de Jéroboam qui sera mis dans un sépulcre, parce qu’il est le seul de la maison de Jéroboam en qui se soit trouvé quelque chose de bon devant Yahweh, le Dieu d’Israël.
Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
14 Yahweh établira sur Israël un roi qui exterminera la maison de Jéroboam ce jour-là. Mais quoi? Déjà la chose arrive!
“Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
15 Yahweh frappera Israël, comme le roseau est agité au sein des eaux; il arrachera Israël de ce bon pays qu’il avait donné à leurs pères, et il les dispersera de l’autre côté du fleuve, parce qu’ils se sont fait des aschérahs, irritant Yahweh.
Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
16 Il livrera Israël à cause des péchés de Jéroboam qu’il a commis et qu’il a fait commettre à Israël. »
Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
17 La femme de Jéroboam se leva et, s’étant mise en route, elle arriva à Thersa. Comme elle franchissait le seuil de la maison, l’enfant mourut.
Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
18 On l’enterrera, et tout Israël le pleura, selon la parole que Yahweh avait dite par l’organe de son serviteur Ahias, le prophète.
Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
19 Le reste des actes de Jéroboam, comment il fit la guerre et comment il régna, voici que cela est écrit dans le livre des Chroniques des rois d’Israël.
Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
20 Le temps que régna Jéroboam fut de vingt-deux ans, et il se coucha avec ses pères. Nadab, son fils, régna à sa place.
Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Roboam, fils de Salomon, régna en Juda. Il avait quarante et un ans lorsqu’il devint roi, et il régna dix-sept ans à Jérusalem, la ville que Yahweh avait choisie parmi toutes les tribus d’Israël pour y mettre son nom. Sa mère s’appelait Naama, l’Ammonite.
Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
22 Juda fit ce qui est mal aux yeux de Yahweh et, par les péchés qu’ils commirent, ils excitèrent sa jalousie plus que ne l’avaient fait leurs pères.
Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
23 Ils se bâtirent, eux aussi, des hauts lieux avec des stèles et des aschérahs, sur toute colline élevée et sous tout arbre vert.
Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
24 Il y eut même des prostitués dans le pays. Ils agirent selon toutes les abominations des nations que Yahweh avait chassées devant les enfants d’Israël.
Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
25 La cinquième année du règne de Roboam, Sésac, roi d’Égypte, monta contre Jérusalem.
A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
26 Il prit les trésors de la maison de Yahweh et les trésors de la maison du roi: il prit tout. Il prit tous les boucliers d’or que Salomon avait faits.
Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
27 A leur place, le roi Roboam fit des boucliers d’airain, et il les remit aux mains des chefs des coureurs qui gardaient l’entrée de la maison du roi.
Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
28 Chaque fois que le roi allait à la maison de Yahweh, les coureurs les portaient; et ils les rapportaient ensuite dans la chambre des coureurs.
Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
29 Le reste des actes de Roboam, et tout ce qu’il a fait, cela n’est-il pas écrit dans le livre des Chroniques des rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
30 Il y eut toujours guerre entre Roboam et Jéroboam.
Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
31 Roboam se coucha avec ses pères, et il fut enterré avec ses pères dans la ville de David. Sa mère s’appelait Naama, l’Ammonite; et Abiam, son fils, régna à sa place.
Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 1 Rois 14 >