< 1 Chroniques 17 >

1 Lorsque David fut établi dans sa maison, David dit à Nathan le prophète: « Voici que j’habite dans une maison de cèdre, et l’arche de l’alliance de Yahweh est sous la tente! »
Bayan Dawuda ya zauna a fadansa, sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar da aka yi da al’ul, yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yana a ƙarƙashin tenti.”
2 Nathan répondit à David: « Fais ce que tu as dans le cœur, car Dieu est avec toi. »
Natan ya amsa wa Dawuda ya ce, “Duk abin da kake tunani a zuciya, ka yi, gama Allah yana tare da kai.”
3 Cette nuit-là, la parole de Dieu fut adressée à Nathan en ces termes:
A daren nan maganar Allah ta zo wa Natan cewa,
4 « Va dire à David, mon serviteur: Ainsi parle Yahweh: Ce n’est pas toi qui me bâtiras une maison pour que j’y habite.
“Ka tafi ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ba kai ba ne za ka gida mini gidan da zan zauna a ciki.
5 Car je n’ai pas habité dans une maison, depuis le jour où j’ai fait monter Israël d’Égypte jusqu’à ce jour; mais j’ai été de tente en tente et de demeure en demeure.
Ban taɓa zama a gida daga ranar da na fito da Isra’ila daga Masar ba har wa yau. Na yi ta yawo daga gefen da aka kafa tenti zuwa wani, daga wannan wuri zuwa wancan.
6 Pendant tout le temps que j’ai voyagé avec tout Israël, ai-je dit un mot à l’un des juges d’Israël à qui j’ai ordonné de paître mon peuple, en disant: Pourquoi ne me bâtissez-vous pas une maison de cèdre?
Duk inda na tafi tare da Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani daga cikin shugabanninsu waɗanda na umarta su yi kiwon mutanena, “Don me ba ku gida mini gidan al’ul ba?”’
7 Maintenant, tu diras à mon serviteur, à David: Ainsi parle Yahweh des armées: Je t’ai pris au pâturage, derrière les brebis, pour être prince sur mon peuple d’Israël;
“Yanzu, ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauke ka daga makiyaya da kuma daga bin garke, don ka zama mai mulki a bisa mutanena Isra’ila.
8 j’ai été avec toi partout où tu allais, j’ai exterminé tous tes ennemis devant toi, et je t’ai fait un nom comme le nom des grands qui sont sur la terre.
Na kasance tare da kai ko’ina ka tafi, na kuma yanke dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka kamar sunayen mutane mafi girma na duniya.
9 J’ai assigné un lieu à mon peuple d’Israël, et je l’ai planté, et il habite chez lui, et il ne sera plus troublé, et les fils d’iniquité ne l’opprimeront plus, comme autrefois
Zan kuma tanada wuri domin mutanena Isra’ila, zan kuma kafa su saboda za su kasance da gidan kansu ba kuwa za a ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara zaluntar su ba, yadda suka yi da farko
10 et comme au jour où j’avais établi des juges sur mon peuple d’Israël. J’ai humilié tous tes ennemis. Et je t’annonce que Yahweh te bâtira une maison.
da kuma suka yi tun lokacin da na sa shugabanni a bisa mutanen Isra’ila. Zan rinjaye dukan abokan gābanka. “‘Na furta maka cewa Ubangiji zai gina maka gida,
11 Quand tes jours seront accomplis et que tu iras avec tes pères, j’élèverai ta postérité après toi, l’un de tes fils, et j’affermirai son règne.
sa’ad da kwanakinka suka ƙare ka kuma tafi don ka kasance da kakanninka, zan tā da ɗaya cikin’ya’yanka maza, daga zuriyarka yă gāje ka, zan kuma kafa mulkinka.
12 C’est lui qui me bâtira une maison, et j’affermirai son trône pour toujours.
Shi ne zai gina gida domina, zan kuma kafa sarautarsa har abada.
13 Je serai pour lui un père, et il sera pour moi un fils; et je ne lui retirerai pas ma grâce, comme je l’ai retirée à celui qui a régné avant toi.
Zan zama Ubansa, zai kuma zama ɗana. Ba zan taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi, kamar yadda na ɗauke ta daga wanda ya riga ka ba.
14 Je l’établirai pour toujours dans ma maison et dans mon royaume, et son trône sera affermi pour toujours. »
Zan sa shi a bisa gidana da mulkina har abada; kujerar sarautarsa za tă kahu har abada.’”
15 Nathan parla à David selon toutes ces paroles et toute cette vision.
Natan ya faɗa wa Dawuda dukan kalmomin wahayin nan.
16 Et le roi David vint et demeura devant Yahweh; et il dit: « Qui suis-je, Yahweh Dieu, et quelle est ma maison pour que vous m’ayez fait arriver jusque-là?
Sai Sarki Dawuda ya shiga ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, kuma wane ne iyalina, da ka kawo ni har zuwa nan?
17 Et c’est encore peu de chose à vos yeux, ô Dieu! Vous avez parlé de la maison de votre serviteur pour les temps lointains, et vous m’avez regardé comme un homme de haut rang, ô Yahweh Dieu.
Kuma sai ka ce wannan bai isa ba a idonka, ya Allah, ka yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Ka dube ni sai ka ce ni ne mafi ɗaukaka cikin mutane, ya Ubangiji Allah.
18 Que pourrait vous dire de plus David sur l’honneur accordé à votre serviteur? Vous connaissez votre serviteur.
“Me kuma Dawuda zai ce maka saboda girmamawar da ka yi wa bawanka? Gama ka san bawanka,
19 Yahweh, c’est à cause de votre serviteur et selon votre cœur, que vous avez fait toute cette grande chose, pour faire connaître toutes ces grandes choses.
Ya Ubangiji. Gama saboda bawanka da kuma bisa ga nufinka, ka yi wannan babban abu, ka kuma sanar da dukan manyan alkawura.
20 Yahweh, nul n’est semblable à vous, et il n’y a pas d’autre Dieu que vous, d’après tout ce que nous avons entendu de nos oreilles.
“Babu wani kamar ka, ya Ubangiji, babu kuma Allah sai kai, kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
21 Quelle autre nation y a-t-il sur la terre comme votre peuple d’Israël, que Dieu est venu racheter pour en faire son peuple, pour vous faire un nom par des choses grandes et des prodiges, en chassant des nations de devant votre peuple que vous avez racheté de l’Égypte?
Wane ne kuma yake kamar mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allahnta ya fita don yă fanshi mutane wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa masu banmamaki masu banrazana ta wurin korin al’ummai daga gaban mutanenka, waɗanda ka fansa daga Masar?
22 Vous avez fait de votre peuple d’Israël votre peuple à jamais, et vous, Yahweh, vous êtes devenu son Dieu.
Ka mai da mutanenka Isra’ila na kanka har abada, kuma kai, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
23 Maintenant, Yahweh, que la parole que vous avez dite au sujet de votre serviteur et au sujet de sa maison subsiste à jamais, et agissez selon votre parole!
“Yanzu kuwa, Ubangiji, bari alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa yă kahu har abada. Yi kamar yadda ka yi alkawari,
24 Qu’elle subsiste, et que votre nom soit glorifié à jamais, et que l’on dise: Yahweh des armées, le Dieu d’Israël, est Dieu pour Israël! Et que la maison de David, votre serviteur, soit affermie devant vous!
saboda zai kahu kuma sunanka zai zama mai girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah a bisa Isra’ila, Allahn Isra’ila ne!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
25 Car vous-même, ô mon Dieu, vous avez révélé à votre serviteur que vous lui bâtiriez une maison; c’est pourquoi votre serviteur a osé prier devant vous.
“Kai, Allahna, ka bayyana ga bawanka cewa za ka gina gida dominsa. Ta haka bawanka ya sami ƙarfin gwiwa ya yi addu’a gare ka.
26 Maintenant, Yahweh, c’est vous qui êtes Dieu, et vous avez dit à votre serviteur cette parole agréable.
Ya Ubangiji, kai ne Allah! Ka yi alkawari abubuwa masu kyau wa bawanka.
27 Maintenant, il vous a plu de bénir la maison de votre serviteur, afin qu’elle subsiste à jamais devant vous; car ce que vous bénissez, Yahweh, est béni pour toujours. »
Yanzu ka ji daɗi don ka albarkace gidan bawanka, don yă ci gaba har abada a gabanka; gama kai, ya Ubangiji, ka albarkace shi, ya kuma sami albarka ke nan har abada.”

< 1 Chroniques 17 >