< 1 Chroniques 12 >

1 Voici ceux qui vinrent vers David à Siceleg, lorsqu’il devait encore se tenir éloigné de la face de Saül, fils de Cis; ils étaient parmi les vaillants qui le secoururent pendant la guerre.
Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
2 C’étaient des archers, exercés à lancer des pierres de la main droite et de la main gauche, et à tirer des flèches avec leur arc; ils étaient d’entre les frères de Saül, de Benjamin.
suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
3 A leur tête Ahiéser, puis Joas, tous deux fils de Samaa, de Gabaa; Jaziel et Phallet, fils d’Azmoth; Baracha; Jéhu, d’Anatoth;
Ahiyezer babbansu da Yowash’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya; Yeziyel da Felet’ya’yan Azmawet; Beraka, Yehu daga Anatot,
4 Samaïas, de Gabaon, vaillant parmi les Trente et chef des Trente; Jérémie; Jéhéziel; Johanan; Jézabad, de Gédéra;
da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin; Irmiya, Yahaziyel, Yohanan, Yozabad daga Gedera,
5 Eluzaï; Jérimuth; Baalia; Samaria; Saphatia, de Haruph;
Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
6 Elcana, Jésia, Azaréel, Joéser et Jesbaam, fils de Coré;
Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
7 Joéla et Zabadia, fils de Jéroham, de Gédor.
da Yoyela da Zebadiya’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
8 Parmi les Gadites, des hommes vaillants passèrent auprès de David, dans les lieux forts, au désert: guerriers exercés au combat, sachant manier le bouclier et la lance, ayant un aspect de lions, aussi agiles que des gazelles sur les montagnes.
Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
9 Ezer était le chef; Obdias, le second; Eliab, le troisième;
Ezer shi ne babba, Obadiya shi ne mai binsa a shugabanci, Eliyab na uku,
10 Masmana, le quatrième; Jérémie, le cinquième;
Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
11 Ethi, le sixième; Eliel, le septième;
Attai na shida, Eliyel na bakwai,
12 Johanan, le huitième; Elzébad, le neuvième;
Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
13 Jérémie, le dixième; Machbanaï, le onzième.
Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
14 C’étaient des fils de Gad, chefs de l’armée; un seul, le plus petit, pouvait l’emporter sur cent, et le plus grand sur mille.
Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
15 Ce sont eux qui passèrent le Jourdain au premier mois, alors qu’il déborde sur toutes ses rives, et qui mirent en fuite tous les habitants des vallées, à l’orient et à l’occident.
Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
16 Des fils de Benjamin et de Juda vinrent vers David, dans les lieux forts.
Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
17 David sortit au-devant d’eux, prit la parole, et leur dit: « Si vous êtes venus à moi avec des sentiments pacifiques, pour me secourir, mon cœur se portera vers vous, en vue de nous unir; mais si c’est pour me livrer perfidement à mes ennemis, lorsque aucune violence ne s’attache à mes mains, que le Dieu de nos pères le voie et qu’il fasse justice! »
Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
18 L’Esprit revêtit Amasaï, chef des Trente, et il dit: « A toi, David, et avec toi, fils d’Isaï! Paix, paix à toi, et paix à celui qui te secourt, car ton Dieu t’a secouru! » Et David les accueillit et les plaça parmi les chefs de la bande.
Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce, “Mu naka ne, ya Dawuda! Muna tare da kai, ya ɗan Yesse! Nasara, nasara gare ka, nasara kuma ga waɗanda suke taimakonka. Gama Allahnka zai taimake ka.” Saboda haka Dawuda ya karɓe su ya kuma mai da su shugabannin ƙungiyoyin maharansa.
19 Des hommes de Manassé se joignirent à David, lorsqu’il alla avec les Philistins faire la guerre à Saül. Mais ils ne secoururent pas les Philistins; car les princes des Philistins renvoyèrent à dessein David en disant: « Au péril de nos têtes, il joindrait son maître Saül. »
Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
20 Comme il revenait à Siceleg, des hommes de Manassé se joignirent à lui: Ednas, Jozabad, Jédihel, Michaël, Jozabad, Eliu et Salathi, chefs des milliers de Manassé.
Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
21 Ils secoururent David contre les bandes, car ils étaient tous des vaillants, et ils furent chefs dans l’armée.
Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
22 Et de jour en jour des hommes arrivaient auprès de David pour le secourir, jusqu’à ce qu’il eût une grande armée, comme une armée de Dieu.
Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
23 Voici le nombre des chefs des hommes armés pour la guerre qui vinrent auprès de David à Hébron, pour lui transférer la royauté de Saül, selon l’ordre de Yahweh.
Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
24 Fils de Juda, portant le bouclier et la lance, six mille huit cents, armés pour la guerre. —
Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
25 Des fils de Siméon, hommes vaillants à la guerre, sept mille cent. —
mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
26 Des fils de Lévi, quatre mille six cents;
mutanen Lawi, su 4,600,
27 et Joïada, chef de la famille d’Aaron, et avec lui trois mille sept cents;
haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
28 et Sadoc, jeune homme vaillant, et la maison de son père, vingt-deux chefs. —
da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
29 Des fils de Benjamin, frères de Saül, trois mille; car jusqu’alors la plus grande partie d’entre eux gardaient fidélité à la maison de Saül. —
mutanen Benyamin,’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
30 Des fils d’Ephraïm, vingt mille huit cents, hommes vaillants et renommés dans les maisons de leurs pères. —
mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
31 De la demi-tribu de Manassé, dix-huit mille, qui furent nominativement désignés pour aller établir David roi. —
mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
32 Des fils d’Issachar, ayant l’intelligence des temps pour savoir ce que devait faire Israël, deux cents chefs, et tous leurs frères sous leurs ordres. —
mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
33 De Zabulon, cinquante mille, en état d’aller à l’armée, prêts à la guerre et en parfait équipement de guerre, pour se ranger en bataille d’un cœur résolu. —
mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
34 De Nephthali, mille chefs, et avec eux trente-sept mille, portant le bouclier et la lance. —
mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
35 Des Danites prêts à la guerre, vingt-huit mille six cents. —
mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
36 D’Aser, en état d’aller à l’armée et prêts à la guerre, quarante mille. —
mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
37 Et de l’autre coté du Jourdain, des Rubenites, des Gadites et de la demi-tribu de Manassé, en parfait équipement d’armes de guerre, cent vingt mille.
kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
38 Tous ces hommes de guerre, sachant se ranger en bataille, vinrent d’un cœur sincère à Hébron pour établir David roi sur tout Israël; et tout le reste d’Israël n’avait également qu’un cœur pour établir David roi.
Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima. Suka zo Hebron da cikakken niyya don su naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila. Duka sauran Isra’ilawa su ma suka goyi baya a naɗa Dawuda sarki.
39 Ils furent là trois jours avec David, mangeant et buvant, car leurs frères leur avaient préparé des provisions.
Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
40 Et même ceux qui habitaient près d’eux, jusqu’à Issachar, à Zabulon et à Nephthali, apportaient des vivres sur des ânes, sur des chameaux, sur des mulets et sur des bœufs, des provisions de farine, des masses de figues sèches et des raisins secs, du vin, de l’huile, des bœufs et des brebis en abondance; car il y avait joie en Israël.
Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.

< 1 Chroniques 12 >