< Sophonie 3 >

1 Malheur à celle qui est rebelle et souillée, à la ville oppressive!
Taki ta ƙare, ke birnin mai danniya, mai’yan tawaye da kuma masu ƙazanta!
2 Elle n'a pas obéi à la voix. Elle n'a pas reçu de correction. Elle ne s'est pas confiée à Yahvé. Elle ne s'est pas approchée de son Dieu.
Ba kya yi wa kowa biyayya, ba kya kuma yarda da kuskurenki. Ba kya dogara ga Ubangiji, ba kya kuma kusatowa kusa da Allahnki.
3 Ses princes sont des lions rugissants. Ses juges sont des loups du soir. Ils ne laissent rien au lendemain.
Sarakunanki ruri ne na zakoki, shugabanninki kyarketan dare ne, waɗanda ba sa rage kome don safe.
4 Ses prophètes sont des gens arrogants et perfides. Ses prêtres ont profané le sanctuaire. Ils ont fait violence à la loi.
Annabawanki mahaukata ne mutanenki masu cin amana ne. Firistocinki suna ƙazantar da Wurin Mai Tsarki suna kuma keta dokoki.
5 Yahvé, en elle, est juste. Il ne fait pas de mal. Chaque matin, il fait éclater sa justice. Il ne faillit pas, mais les injustes ne connaissent pas la honte.
Ubangiji da yake cikinki mai adalci ne; ba ya yin abin da ba daidai ba. Kowace safiya yakan bayyana dokokinsa a fili, kowace sabuwar rana kuma ba ya kāsawa, duk da haka marasa adalci ba sa jin kunya.
6 J'ai exterminé des nations. Leurs remparts sont désolés. J'ai rendu leurs rues désertes, pour que personne n'y passe. Leurs villes sont détruites, il n'y a plus d'homme, il n'y a plus d'habitant.
“Na daddatse al’ummai; an kuma rurrushe kagararsu. Na bar titunansu ba kowa, ba mai ratsawa a ciki. An ragargaza biranensu; ba wanda za a bari, babu ko ɗaya.
7 J'ai dit: « Crains-moi seulement. Recevez la correction », afin que sa demeure ne soit pas anéantie, selon tout ce que j'ai prévu à son sujet. Mais ils se sont levés de bonne heure et ont corrompu toutes leurs actions.
Na ce wa birnin, ‘Tabbatacce za ki ji tsorona ki kuma yarda da gyara!’ Ta haka ba za a datse wurin zamanki ba, ba kuwa dukan hukuncena za su hau bisa kansu ba. Amma har yanzu suna marmari su yi rashin gaskiya a duk abin da suke yi.
8 « Attendez-moi donc », dit Yahvé, « jusqu'au jour où je me lèverai sur la proie, car ma résolution est de rassembler les nations, d'assembler les royaumes pour répandre sur eux ma fureur, toute mon ardente colère, car toute la terre sera dévorée par le feu de ma jalousie ».
Saboda haka ku jira ni,” in ji Ubangiji; “a ranar da zan tsaya in ba da shaida, Na yanke shawara in tattara dukan al’ummai, in tattara mulkoki in kuma zuba fushina a kansu, da dukan zafin haushina. Za a mamaye dukan duniya da zafin fushina.
9 Car alors je purifierai les lèvres des peuples, afin qu'ils invoquent tous le nom de Yahvé, pour le servir épaule contre épaule.
“Sa’an nan zan tsarkake leɓunan mutanen, don dukansu su kira bisa ga sunan Ubangiji su kuma yi masa hidima kafaɗa da kafaɗa.
10 De l'autre côté des fleuves de Cusch, mes adorateurs, les filles de mon peuple dispersé, apporteront mon offrande.
Tun daga ƙetaren rafuffukan Kush masu yi mini sujada, mutanena da suke a warwatse, za su kawo mini hadayu.
11 En ce jour-là, vous ne serez pas déçus pour toutes les actions que vous avez commises contre moi; car alors j'ôterai du milieu de vous vos orgueilleux, et vous ne serez plus arrogants sur ma montagne sainte.
A wannan rana ba za ku sha kunya saboda laifofin da kuka yi mini, gama zan ɗauke wa wannan birni waɗanda suke farin ciki cikin girmankansu. Ba kuma za ka ƙara yin kallon reni a tuduna mai tsarki ba.
12 Mais je laisserai parmi vous un peuple affligé et pauvre, et il se réfugiera dans le nom de l'Éternel.
Amma zan zauna a cikinki masu tawali’u da masu ƙasƙantar da kai, waɗanda suke dogara ga sunan Ubangiji.
13 Le reste d'Israël ne commettra pas d'iniquité, ne dira pas de mensonges, et il ne se trouvera pas de langue mensongère dans leur bouche; ils paîtront et se coucheront, et personne ne leur fera peur. »
Raguwar Isra’ila ba za su ƙara aikata abin da ba daidai ba, ba za su faɗa ƙarya ba, ba kuwa za a sami ruɗu a bakunansu ba. Za su ci su kuma kwanta kuma babu wanda zai ba su tsoro.”
14 Chante, fille de Sion! Crie, Israël! Sois dans l'allégresse et réjouis-toi de tout ton cœur, fille de Jérusalem!
Ki rera, ya Diyar Sihiyona; ki tā da murya, ya Isra’ila! Ki yi murna ki kuma yi farin ciki da dukan zuciyarki, Ya Diyar Urushalima!
15 L'Éternel a ôté tes jugements, Il a chassé ton ennemi. Il a chassé ton ennemi. Le roi d'Israël, Yahvé, est au milieu de toi. Tu ne craindras plus le mal.
Ubangiji ya ɗauke hukuncinki, ya mai da abokan gābanki baya. Ubangiji, Sarkin Isra’ila, yana tare da ke; ba kuma za ki ƙara jin tsoron wani lahani ba.
16 En ce jour-là, on dira à Jérusalem: « Ne crains pas, Sion. Ne laisse pas tes mains s'affaiblir. »
A wannan rana za su cewa Urushalima, “Kada ki ji tsoro, ya Sihiyona; kada ki bar hannuwanki su raunana.
17 Yahvé, ton Dieu, est au milieu de toi, un puissant qui sauve. Il se réjouira de toi dans l'allégresse. Il te calmera dans son amour. Il se réjouira de toi en chantant.
Ubangiji Allahnki yana tare da ke, mai iko ne don ceto. Zai yi matuƙar farin ciki da ke, zai rufe ki da ƙaunarsa, zai yi farin ciki da ke ta wurin rerawa.”
18 J'éloignerai de toi ceux qui s'affligent au sujet des fêtes fixées. Ils sont pour toi un fardeau et un opprobre.
“Zan cire taƙaici daga gare ki a ƙayyadaddun bukukkuwa; su kaya ne da kuma zargi a gare ki.
19 Voici, en ce temps-là, je m'occuperai de tous ceux qui t'affligent, je sauverai les boiteux et je rassemblerai ceux qui ont été chassés. Je leur donnerai la louange et l'honneur, eux dont la honte a été dans toute la terre.
A wannan lokaci zan jijji wa waɗanda suka danne ku; zan kuɓutar da guragu in kuma tattara waɗanda suke a warwatse. Zan sa a yabe su a kuma girmama su a kowace ƙasar da aka kunyatar da su.
20 En ce temps-là, je vous ferai entrer, et en ce temps-là, je vous rassemblerai, car je vous rendrai honneur et louange parmi tous les peuples de la terre, quand je rétablirai votre fortune sous vos yeux, dit l'Éternel.
A wannan lokaci zan tattara ku; a wannan lokaci zan kawo ku gida, zan sa a yabe ku a kuma girmama ku a cikin dukan mutanen duniya a sa’ad da na maido da arzikinku a idanunku,” in ji Ubangiji.

< Sophonie 3 >