< Zacharie 7 >

1 La quatrième année du roi Darius, la parole de Yahvé fut adressée à Zacharie, le quatrième jour du neuvième mois, le mois de Chislev.
A shekara ta huɗu ta Sarki Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa Zakariya a rana ta huɗu ta watan tara, wato, watan Kisleb.
2 Le peuple de Béthel envoya Sharezer, Regem Melech et leurs hommes pour implorer la faveur de Yahvé,
Mutanen Betel sun aika Sharezer da Regem-Melek, tare da mutanensu su nemi tagomashin Ubangiji
3 et pour parler aux prêtres de la maison de Yahvé des armées et aux prophètes, en disant: « Devrais-je pleurer au cinquième mois, en me séparant, comme je l'ai fait pendant tant d'années? »
ta wurin tambayar firistocin da kuma annabawan gidan Ubangiji Maɗaukaki, “Ko ya kamata in yi makoki da azumi a wata na biyar, yadda na yi a shekaru masu yawa?”
4 Alors la parole de Yahvé des armées me fut adressée en ces termes:
Sai maganar Ubangiji Maɗaukaki ta zo mini ta ce,
5 Parle à tout le peuple du pays et aux prêtres, et dis: « Lorsque vous avez jeûné et pleuré au cinquième et au septième mois pendant ces soixante-dix ans, n'avez-vous pas jeûné pour moi, vraiment pour moi?
“Ka tambayi dukan mutanen ƙasar da firistoci cewa, ‘Sa’ad da kuka yi makoki da azumi a wata na biyar da na bakwai dukan shekaru saba’in nan, a ainihi saboda ni kuka yi azumi?
6 Quand vous mangez et quand vous buvez, ne mangez-vous pas pour vous-mêmes et ne buvez-vous pas pour vous-mêmes?
Kuma sa’ad da kuke ci kuke sha, ba kanku kuke yi wa shagali ba?
7 Ne sont-ce pas là les paroles que Yahvé a annoncées par les anciens prophètes, lorsque Jérusalem était habitée et prospère, ainsi que les villes qui l'entouraient, et que le Sud et la plaine étaient habités? ».
Ashe, ba kalmomin da Ubangiji ya faɗi ke nan ta bakin annabawan farko ba sa’ad da Urushalima da garuruwan da suke kewaye da ita suke hutawa, suke cikin wadata, akwai kuma mutane a Negeb da yammancin gindin tuddai?’”
8 La parole de Yahvé fut adressée à Zacharie, en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta sāke zuwa wa Zakariya cewa,
9 Yahvé des armées a parlé ainsi: « Pratiquez un jugement équitable, et ayez de la bonté et de la compassion pour votre frère.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku yi shari’ar gaskiya; ku nuna jinƙai da tausayi ga juna.
10 N'opprimez pas la veuve, ni l'orphelin, ni l'étranger, ni le pauvre; et qu'aucun de vous ne médite dans son cœur le mal contre son frère.
Kada ku danne gwauruwa ko maraya, baƙo ko talaka. A cikin zuciyarku kada ku yi mugun tunani game da juna.’
11 Mais ils refusèrent d'écouter, ils tournèrent le dos et bouchèrent leurs oreilles pour ne pas entendre.
“Amma suka ƙi su saurara; da taurinkai suka juya bayansu suka kuma toshe kunnuwansu.
12 Oui, ils ont rendu leur cœur dur comme du silex, de peur d'entendre la loi et les paroles que Yahvé des armées avait envoyées par son Esprit par les anciens prophètes. C'est pourquoi une grande colère est venue de l'Éternel des armées.
Suka taurare zukatansu kamar dutse, suka ƙi jin abin da doka ko kuma maganar Ubangiji Maɗaukaki take faɗi wadda ya aika ta wurin Ruhunsa ta wurin annabawan farko. Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ji fushi ƙwarai.
13 De même qu'il a appelé et qu'ils ont refusé d'écouter, de même ils appelleront et je n'écouterai pas, dit Yahvé des armées,
“‘Sa’ad da na yi kira, ba su saurara ba; saboda haka sa’ad da suka kira, ba zan saurara ba,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
14 mais je les disperserai dans un tourbillon parmi toutes les nations qu'ils n'ont pas connues. C'est ainsi que le pays a été dévasté après eux, de sorte que personne n'y passait ni n'y retournait, car ils ont rendu désolant le pays agréable. »
‘Na warwatsar da su da guguwa a cikin dukan ƙasashe, inda suka zama baƙi. Aka bar ƙasar ta zama kango bayansu, da har ba mai shiga ko fita. Haka suka sa ƙasan nan mai daɗi ta zama kango.’”

< Zacharie 7 >