< Zacharie 14 >

1 Voici venir un jour de Yahvé, où votre butin sera partagé au milieu de vous.
Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
2 Car je rassemblerai toutes les nations contre Jérusalem pour qu'elles combattent; la ville sera prise, les maisons pillées, les femmes violées. La moitié de la ville partira en captivité, et le reste du peuple ne sera pas retranché de la ville.
Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
3 Alors Yahvé sortira et combattra contre ces nations, comme au jour du combat.
Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
4 Ses pieds se tiendront en ce jour-là sur la montagne des Oliviers, qui est devant Jérusalem à l'est; et la montagne des Oliviers se fendra en deux d'est en ouest, formant une très grande vallée. La moitié de la montagne se déplacera vers le nord, et l'autre moitié vers le sud.
A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
5 Vous fuirez par la vallée de mes montagnes, car la vallée des montagnes s'étendra jusqu'à Azel. Oui, vous fuirez, comme vous avez fui avant le tremblement de terre, à l'époque d'Ozias, roi de Juda. Yahvé mon Dieu viendra, et tous les saints avec vous.
Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
6 Il arrivera en ce jour-là qu'il n'y aura ni lumière, ni froid, ni gelée.
A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
7 Ce sera un jour unique, connu de Yahvé - ni jour, ni nuit - mais il arrivera qu'à l'heure du soir il y aura de la lumière.
Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
8 En ce jour-là, des eaux vives sortiront de Jérusalem, pour moitié vers la mer orientale et pour moitié vers la mer occidentale. Il en sera ainsi en été et en hiver.
A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
9 Yahvé sera roi sur toute la terre. En ce jour-là, Yahvé sera unique, et son nom sera unique.
Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
10 Tout le pays sera rendu semblable à la plaine, depuis Guéba jusqu'à Rimmon, au sud de Jérusalem; elle s'élèvera et habitera à sa place, depuis la porte de Benjamin jusqu'à la place de la première porte, jusqu'à la porte d'angle, et depuis la tour de Hananel jusqu'aux pressoirs du roi.
Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
11 Les hommes y habiteront, et il n'y aura plus de malédiction; mais Jérusalem habitera en sécurité.
Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
12 Voici la plaie dont Yahvé frappera tous les peuples qui auront combattu contre Jérusalem: leur chair se consumera pendant qu'ils se tiendront sur leurs pieds, leurs yeux se consumeront dans leurs orbites, et leur langue se consumera dans leur bouche.
Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
13 En ce jour-là, il y aura parmi eux une grande panique de la part de l'Éternel; chacun saisira la main de son prochain, et sa main se lèvera contre la main de son prochain.
A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
14 Juda aussi combattra à Jérusalem; et les richesses de toutes les nations d'alentour seront rassemblées: or, argent et vêtements, en grande abondance.
Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
15 Une telle plaie tombera sur le cheval, sur la mule, sur le chameau, sur l'âne et sur tous les animaux qui seront dans ces camps.
Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
16 Il arrivera que tous ceux qui resteront de toutes les nations qui sont venues contre Jérusalem monteront d'année en année pour se prosterner devant le roi, l'Yahvé des armées, et pour célébrer la fête des tentes.
Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
17 Celui de toutes les familles de la terre qui ne montera pas à Jérusalem pour se prosterner devant le roi, l'Éternel des armées, celui-là ne recevra pas de pluie.
In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
18 Si la famille d'Égypte ne monte pas et ne vient pas, il ne pleuvra pas non plus sur elle. Ce sera la plaie dont Yahvé frappera les nations qui ne monteront pas pour célébrer la fête des tabernacles.
In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
19 Ce sera le châtiment de l'Égypte et le châtiment de toutes les nations qui ne monteront pas pour célébrer la fête des kermesses.
Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
20 En ce jour-là, on inscrira sur les cloches des chevaux: « SAINTETÉ À YAHVÉ »; et les marmites de la maison de Yahvé seront comme les coupes devant l'autel.
A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
21 Oui, toutes les marmites de Jérusalem et de Juda seront consacrées à l'Éternel des armées; et tous ceux qui sacrifient viendront s'en servir et cuisineront dedans. En ce jour-là, il n'y aura plus de Cananéen dans la maison de l'Éternel des armées.
Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.

< Zacharie 14 >