< Psaumes 89 >

1 Une contemplation par Ethan, l'Ezrahite. Je chanterai à jamais la bonté de Yahvé. De ma bouche, je ferai connaître ta fidélité à toutes les générations.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Je déclare en effet: « L'amour tient bon pour toujours. Tu as établi les cieux. Ta fidélité est en eux. »
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 « J'ai fait une alliance avec mon élu, J'ai juré à David, mon serviteur,
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 J'établirai ta descendance pour toujours, et rebâtir ton trône pour toutes les générations. (Selah)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 Les cieux célèbrent tes merveilles, Yahvé, ta fidélité aussi dans l'assemblée des saints.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Car qui, dans les cieux, peut être comparé à Yahvé? Qui, parmi les fils des êtres célestes, est semblable à Yahvé,
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 un Dieu très impressionnant dans le conseil des saints, à être craint de tous ceux qui l'entourent?
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 Yahvé, Dieu des armées, qui est un puissant, comme toi? Yah, ta fidélité est autour de toi.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Tu domines l'orgueil de la mer. Quand ses vagues se soulèvent, vous les calmez.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Tu as brisé Rahab en morceaux, comme un mort. Tu as dispersé tes ennemis avec ton bras puissant.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 Les cieux sont à toi. La terre aussi est à vous, le monde et sa plénitude. Vous les avez fondés.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Tu as créé le nord et le sud. Le Thabor et l'Hermon se réjouissent en ton nom.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Tu as un bras puissant. Ta main est forte, et ta droite est exaltée.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 La droiture et la justice sont le fondement de ton trône. La bonté et la vérité vont devant ton visage.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Heureux les gens qui apprennent à t'acclamer. Ils marchent dans la lumière de ta présence, Yahvé.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 En ton nom, ils se réjouissent tout le jour. Dans ta justice, ils sont exaltés.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Car tu es la gloire de leur force. Dans ta faveur, notre cor sera exalté.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Car notre bouclier appartient à Yahvé, notre roi au Saint d'Israël.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Puis tu as parlé en vision à tes saints, et dit: « J'ai donné de la force au guerrier. J'ai exalté un jeune homme du peuple.
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 J'ai trouvé David, mon serviteur. Je l'ai oint de mon huile sainte,
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 avec qui ma main s'affermira. Mon bras le renforcera aussi.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 Aucun ennemi ne le taxera. Aucun méchant ne l'opprimera.
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 Je battrai ses adversaires devant lui, et frappe ceux qui le haïssent.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 Mais ma fidélité et ma bonté seront avec lui. En mon nom, sa corne sera exaltée.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Je mettrai aussi sa main sur la mer, et sa main droite sur les rivières.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 Il m'appellera: « Tu es mon Père », mon Dieu, et le rocher de mon salut!
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Je le désigne aussi comme mon premier-né, le plus haut des rois de la terre.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 Je garderai pour lui ma bonté à jamais. Mon alliance restera ferme avec lui.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 Je ferai aussi durer sa descendance à jamais, et son trône comme les jours du ciel.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Si ses enfants abandonnent ma loi, et ne marche pas dans mes ordonnances;
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 s'ils violent mes lois, et ne gardent pas mes commandements;
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 alors je punirai leur péché par la verge, et leur iniquité par des coups.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Mais je ne lui retirerai pas complètement ma bienveillance, ni permettre à ma fidélité de faillir.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 Je ne romprai pas mon alliance, ni altérer ce que mes lèvres ont prononcé.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 J'ai juré une fois par ma sainteté, Je ne mentirai pas à David.
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 Sa descendance durera toujours, son trône comme le soleil devant moi.
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 Il sera établi pour toujours comme la lune, le témoin fidèle dans le ciel. (Selah)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Mais vous avez rejeté et méprisé. Vous avez été en colère contre votre oint.
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Tu as renoncé à l'alliance de ton serviteur. Vous avez souillé sa couronne dans la poussière.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Tu as abattu toutes ses haies. Vous avez détruit ses forteresses.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 Tous ceux qui passent par le chemin le dépouillent. Il est devenu un reproche pour ses voisins.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Tu as élevé la main droite de ses adversaires. Vous avez fait en sorte que tous ses ennemis se réjouissent.
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Oui, tu fais reculer le tranchant de son épée, et ne l'ont pas soutenu dans la bataille.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Tu as mis fin à sa splendeur, et jeté son trône à terre.
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Tu as abrégé les jours de sa jeunesse. Tu l'as couvert de honte. (Selah)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Combien de temps, Yahvé? Allez-vous vous cacher pour toujours? Votre colère brûlera-t-elle comme un feu?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Souviens-toi que mon temps est compté, pour quelle vanité tu as créé tous les enfants des hommes!
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Quel est l'homme qui vivra et ne verra pas la mort? qui délivrera son âme du pouvoir du séjour des morts? (Selah) (Sheol h7585)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
49 Seigneur, où sont tes anciennes bontés, que tu as juré à David dans ta fidélité?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Souviens-toi, Seigneur, de l'opprobre de tes serviteurs, comme je porte dans mon cœur les railleries de tous les peuples puissants,
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 Avec lequel tes ennemis se sont moqués, Yahvé, avec lesquels ils ont tourné en dérision les pas de ton oint.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Bénisoit Yahvé à jamais. Amen, et Amen.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!

< Psaumes 89 >