< Psaumes 88 >

1 Une chanson. Un psaume par les fils de Korah. Pour le chef musicien. Sur l'air de « The Suffering of Affliction ». Une contemplation par Heman, l'Ezrahite. Yahvé, le Dieu de mon salut, J'ai pleuré jour et nuit devant vous.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Que ma prière entre en ta présence. Prêtez l'oreille à mon cri.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Car mon âme est pleine d'angoisse. Ma vie s'approche du séjour des morts. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 Je suis compté parmi ceux qui descendent dans la fosse. Je suis comme un homme qui n'a pas d'aide,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 mis à part parmi les morts, comme les morts qui reposent dans la tombe, dont vous ne vous souvenez plus. Ils sont coupés de ta main.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Tu m'as déposé dans la fosse la plus profonde, dans les profondeurs les plus sombres.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Ta colère pèse sur moi. Tu m'as affligé de toutes tes vagues. (Selah)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Tu m'as enlevé mes amis. Tu as fait de moi une abomination pour eux. Je suis confiné, et je ne peux pas m'échapper.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mes yeux s'assombrissent à cause du chagrin. Je t'ai invoqué chaque jour, Yahvé. J'ai tendu mes mains vers vous.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Faites-vous des prodiges aux morts? Est-ce que les esprits défunts se lèvent et vous louent? (Selah)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Ta bonté est-elle déclarée dans la tombe? Ou votre fidélité dans la Destruction?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Tes merveilles se font-elles connaître dans l'obscurité? Ou ta justice dans le pays de l'oubli?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Mais c'est à toi, Yahvé, que j'ai crié. Le matin, ma prière vient devant vous.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Yahvé, pourquoi rejettes-tu mon âme? Pourquoi me cachez-vous votre visage?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Je suis affligé et prêt à mourir depuis ma jeunesse. Pendant que je souffre de tes terreurs, je suis distrait.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Ton ardente colère s'est abattue sur moi. Vos terreurs m'ont coupé.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Ils m'ont entouré comme de l'eau toute la journée. Ils m'ont complètement englouti.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Tu as éloigné de moi l'amant et l'ami, et mes amis dans les ténèbres.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Psaumes 88 >