< Psaumes 81 >

1 Pour le chef musicien. Sur un instrument de Gath. Par Asaph. Chantez à voix haute à Dieu, notre force! Poussez un cri de joie vers le Dieu de Jacob!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Élevez une chanson, et apportez ici le tambourin, la lyre agréable avec la harpe.
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Sonnez la trompette à la nouvelle lune, à la pleine lune, le jour de notre fête.
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 Car c'est une loi pour Israël, une ordonnance du Dieu de Jacob.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 Il l'a établi en Joseph comme une alliance, quand il a traversé le pays d'Égypte, J'ai entendu une langue que je ne connaissais pas.
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 « J'ai enlevé son épaule du fardeau. Ses mains ont été libérées du panier.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 Tu as appelé dans la détresse, et je t'ai délivré. Je t'ai répondu dans le lieu secret du tonnerre. Je t'ai testé aux eaux de Meribah. (Sélah)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 « Écoute, mon peuple, et je te rendrai témoignage, Israël, si tu m'écoutais!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 Il n'y aura pas de dieu étranger chez vous, et vous n'adorerez aucun dieu étranger.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 Je suis Yahvé, votre Dieu, qui vous a fait sortir du pays d'Égypte. Ouvrez grand votre bouche, et je la remplirai.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 Mais mon peuple n'a pas écouté ma voix. Israël ne voulait pas de moi.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 Je les ai donc laissés aller selon l'obstination de leur cœur, pour qu'ils suivent leurs propres conseils.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 Oh, que mon peuple m'écoute! qu'Israël marche dans mes voies!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 J'allais bientôt soumettre leurs ennemis, et je tournerai ma main contre leurs adversaires.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 Les ennemis de Yahvé s'effaceront devant lui, et leur punition durerait éternellement.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 Mais il les aurait aussi nourris avec le meilleur du blé. Je te rassasierai avec le miel du rocher. »
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”

< Psaumes 81 >