< Psaumes 77 >

1 Pour le chef musicien. À Jeduthun. Un psaume d'Asaph. Mon cri va vers Dieu! En effet, je crie à l'aide de Dieu, et qu'il m'écoute.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 Au jour de ma détresse, j'ai cherché l'Éternel. Ma main a été tendue dans la nuit, et ne s'est pas fatiguée. Mon âme a refusé d'être réconfortée.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 Je me souviens de Dieu, et je gémis. Je me plains, et mon esprit est accablé. (Selah)
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 Tu tiens mes paupières ouvertes. Je suis tellement troublé que je ne peux pas parler.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 J'ai considéré les jours d'autrefois, les années des temps anciens.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 Je me souviens de ma chanson dans la nuit. Je considère dans mon propre cœur; mon esprit s'enquiert diligemment:
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 « Le Seigneur nous rejettera-t-il à jamais? Ne sera-t-il plus favorable?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 Sa bonté s'est-elle évanouie pour toujours? Sa promesse échoue-t-elle pour des générations?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 Dieu a-t-il oublié d'être gracieux? A-t-il, dans sa colère, retenu sa compassion? (Selah)
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 Alors je me suis dit: « Je vais faire appel à cela: les années de la main droite du Très-Haut. »
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 Je me souviendrai des œuvres de l'Éternel; car je me souviendrai de tes merveilles d'antan.
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 Je méditerai aussi sur toute ton œuvre, et considérez vos actions.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 Ton chemin, Dieu, est dans le sanctuaire. Quel dieu est grand comme Dieu?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 Tu es le Dieu qui fait des merveilles. Tu as fait connaître ta force parmi les peuples.
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 Tu as racheté ton peuple par ton bras, les fils de Jacob et de Joseph. (Selah)
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 Les eaux t'ont vu, Dieu. Les eaux t'ont vu, et elles se sont tordues. Les profondeurs se sont également convulsées.
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 Les nuages ont versé de l'eau. Les cieux ont résonné du tonnerre. Vos flèches ont aussi volé autour.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 La voix de ton tonnerre était dans le tourbillon. Les éclairs ont illuminé le monde. La terre a tremblé et a été secouée.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 Ton chemin était à travers la mer, vos chemins à travers les grandes eaux. Vos pas n'étaient pas connus.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 Tu as conduit ton peuple comme un troupeau, par la main de Moïse et d'Aaron.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.

< Psaumes 77 >