< Psaumes 75 >

1 Pour le chef musicien. Sur l'air de « Do Not Destroy ». Un psaume d'Asaph. Une chanson. Nous te rendons grâce, Dieu. Nous rendons grâce, car ton Nom est proche. Les hommes racontent tes merveilles.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
2 Quand je choisis l'heure prévue, Je jugerai de manière irréprochable.
Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
3 La terre et tous ses habitants tremblent. Je tiens fermement ses piliers. (Selah)
Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
4 J'ai dit aux arrogants: « Ne te vante pas! » J'ai dit aux méchants: « N'élevez pas la corne.
Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
5 N'élevez pas votre cor en haut. Ne parlez pas avec un cou raide. »
Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
6 Car ni de l'est, ni de l'ouest, ni encore du sud, vient l'exaltation.
Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
7 Mais Dieu est le juge. Il renverse l'un et relève l'autre.
Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
8 Car il y a une coupe dans la main de Yahvé, pleine de vin mousseux mélangé à des épices. Il le déverse. En effet, les méchants de la terre boivent et le boivent jusqu'à la lie.
A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
9 Mais je le déclarerai à jamais: Je chanterai les louanges du Dieu de Jacob.
Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
10 Je couperai toutes les cornes des méchants, mais les cornes des justes s'élèveront.
wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”

< Psaumes 75 >