< Psaumes 66 >

1 Pour le chef musicien. Un chant. Un psaume. Poussez des cris de joie vers Dieu, sur toute la terre!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Chantez à la gloire de son nom! Offrez la gloire et la louange!
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Dites à Dieu: « Que tes actes sont impressionnants! Par la grandeur de ta puissance, tes ennemis se soumettent à toi.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Toute la terre se prosterne devant toi, et chantera pour vous; ils chanteront ton nom. (Selah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Venez, et voyez les actes de Dieu- un travail impressionnant en faveur des enfants des hommes.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Il a transformé la mer en terre ferme. Ils ont traversé la rivière à pied. Là, nous nous sommes réjouis en lui.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Il domine par sa puissance à jamais. Ses yeux observent les nations. Ne laissez pas les rebelles s'élever contre lui. (Selah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Louez notre Dieu, vous, les peuples! Faites entendre le son de sa louange,
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 qui préserve notre vie parmi les vivants, et ne permet pas à nos pieds d'être déplacés.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Car toi, Dieu, tu nous as mis à l'épreuve. Tu nous as affinés, comme on affine l'argent.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Tu nous as mis en prison. Tu as posé un fardeau sur nos épaules.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Tu as permis à des hommes de chevaucher au-dessus de nos têtes. Nous sommes passés par le feu et par l'eau, mais vous nous avez amené à l'endroit de l'abondance.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 Je viendrai dans ton temple avec des holocaustes. J'accomplirai mes vœux envers toi,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 que mes lèvres ont promis, et ma bouche a parlé, quand j'étais dans la détresse.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Je t'offrirai des holocaustes d'animaux gras, avec l'offrande de béliers, J'offrirai des taureaux avec des chèvres. (Selah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Venez et écoutez, vous tous qui craignez Dieu. Je vais déclarer ce qu'il a fait pour mon âme.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 J'ai crié vers lui avec ma bouche. Je l'ai encensé avec ma langue.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Si j'ai chéri le péché dans mon cœur, le Seigneur n'aurait pas écouté.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 Mais surtout, Dieu a écouté. Il a entendu la voix de ma prière.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Béni soit Dieu, qui n'a pas repoussé ma prière, ni sa gentillesse de ma part.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Psaumes 66 >