< Psaumes 44 >

1 Pour le chef musicien. Par les fils de Korah. Un psaume contemplatif. Nous avons entendu de nos oreilles, Dieu; nos pères nous ont dit quel travail tu as fait de leur temps, dans les jours d'autrefois.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Tu as chassé les nations avec ta main, mais vous les avez plantés. Tu as affligé les peuples, mais vous les diffusez à l'étranger.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 Car ce n'est pas par leur propre épée qu'ils ont pris possession du pays, leur propre bras ne les a pas sauvés non plus; mais ta main droite, ton bras, et la lumière de ton visage, parce que vous leur étiez favorable.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 Dieu, tu es mon Roi. Victoires de commandement pour Jacob!
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Par toi, nous écraserons nos adversaires. Par ton nom, nous écraserons ceux qui se dressent contre nous.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 Car je ne me fierai pas à mon arc, mon épée ne me sauvera pas non plus.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 Mais tu nous as sauvés de nos adversaires, et ont fait honte à ceux qui nous haïssent.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 C'est en Dieu que nous nous sommes glorifiés tout au long du jour. Nous rendrons grâce à ton nom pour toujours. (Selah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 Mais maintenant tu nous as rejetés, et tu nous as déshonorés, et ne sortez pas avec nos armées.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 Tu nous fais reculer devant l'adversaire. Ceux qui nous haïssent prennent le pillage pour eux-mêmes.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 Tu nous as transformés en moutons pour les manger, et nous ont dispersés parmi les nations.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 Vous vendez votre peuple pour rien, et n'ont rien gagné de leur vente.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 Tu fais de nous un objet d'opprobre pour nos voisins, une moquerie et une dérision pour ceux qui nous entourent.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 Tu fais de nous un sujet de discorde parmi les nations, une secousse de la tête parmi les peuples.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 Tout le jour, mon déshonneur est devant moi, et la honte couvre mon visage,
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 à la raillerie de celui qui fait des reproches et abuse verbalement, à cause de l'ennemi et du vengeur.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 Tout cela nous est tombé dessus, mais nous ne vous avons pas oublié. Nous n'avons pas failli à votre alliance.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Notre cœur ne s'est pas détourné, nos pas ne se sont pas écartés de ton chemin,
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 bien que tu nous aies écrasés dans le repaire des chacals, et nous a couverts de l'ombre de la mort.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 Si nous avons oublié le nom de notre Dieu, ou de tendre nos mains vers un dieu étranger,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 Dieu ne va pas chercher ça? Car il connaît les secrets du cœur.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Oui, à cause de toi, on nous tue tout le jour. Nous sommes considérés comme des moutons pour l'abattage.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Réveillez-vous! Pourquoi dors-tu, Seigneur? Debout! Ne nous rejette pas pour toujours.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Pourquoi cachez-vous votre visage, et oublier notre affliction et notre oppression?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 Car notre âme est courbée vers la poussière. Notre corps s'accroche à la terre.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Levez-vous pour nous aider. Rachetez-nous au nom de votre bonté.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Psaumes 44 >