< Psaumes 29 >

1 Un psaume de David. Rendez hommage à Yahvé, fils de puissants, attribuer à Yahvé la gloire et la force.
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Rendez à Yahvé la gloire due à son nom. Adorez Yahvé dans une tenue sacrée.
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 La voix de Yahvé est sur les eaux. Le Dieu de gloire tonne, Yahvé sur les grandes eaux.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 La voix de Yahvé est puissante. La voix de Yahvé est pleine de majesté.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 La voix de Yahvé brise les cèdres. Oui, Yahvé brise en morceaux les cèdres du Liban.
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 Il les fait aussi sauter comme un veau; le Liban et le Sirion comme un jeune bœuf sauvage.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 La voix de Yahvé frappe avec des éclairs.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 La voix de Yahvé fait trembler le désert. Yahvé secoue le désert de Kadesh.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 La voix de Yahvé fait vêler les biches, et dépouille les forêts. Dans son temple, tout dit: « Gloire! »
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 Yahvé était assis sur un trône au moment du déluge. Oui, Yahvé siège comme roi pour toujours.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 Yahvé donnera de la force à son peuple. Yahvé bénira son peuple par la paix.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

< Psaumes 29 >