< Psaumes 147 >

1 Louez Yah, car il est bon de chanter les louanges de notre Dieu; car il est agréable et convenable de le louer.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 Yahvé bâtit Jérusalem. Il rassemble les exclus d'Israël.
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 Il guérit les cœurs brisés, et panse leurs plaies.
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 Il compte le nombre d'étoiles. Il les appelle tous par leur nom.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Grand est notre Seigneur, et puissant en puissance. Sa compréhension est infinie.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 Yahvé soutient les humbles. Il fait tomber les méchants sur le sol.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Chantez à Yahvé avec reconnaissance. Chantez les louanges de notre Dieu sur la harpe,
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 qui couvre le ciel de nuages, qui prépare la pluie pour la terre, qui fait pousser l'herbe sur les montagnes.
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 Il fournit la nourriture pour le bétail, et pour les jeunes corbeaux quand ils appellent.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 Il ne se réjouit pas de la force du cheval. Il ne prend aucun plaisir dans les jambes d'un homme.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 Yahvé prend plaisir à ceux qui le craignent, en ceux qui espèrent en sa bonté.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Loue Yahvé, Jérusalem! Louez votre Dieu, Sion!
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 Car il a renforcé les barres de tes portes. Il a béni vos enfants en vous.
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 Il fait régner la paix dans tes frontières. Il vous remplit avec le meilleur du blé.
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 Il envoie son commandement à la terre. Sa parole court très vite.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 Il donne de la neige comme de la laine, et disperse le givre comme des cendres.
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 Il fait tomber sa grêle comme des cailloux. Qui peut se tenir devant son froid?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 Il envoie sa parole, et les fait fondre. Il fait souffler son vent, et les eaux coulent.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 Il montre sa parole à Jacob, ses lois et ses ordonnances à Israël.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 Il n'a pas fait cela pour n'importe quelle nation. Ils ne connaissent pas ses ordonnances. Louez Yah!
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.

< Psaumes 147 >