< Psaumes 118 >

1 Rendez grâce à Yahvé, car il est bon, car sa bonté est éternelle.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Qu'Israël dise maintenant que sa bonté est éternelle.
Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
3 Que la maison d'Aaron dise maintenant que sa bonté est éternelle.
Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
4 Maintenant, que ceux qui craignent Yahvé disent que sa bonté est éternelle.
Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
5 Dans ma détresse, j'ai invoqué l'Éternel. Yah m'a répondu avec liberté.
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
6 Yahvé est de mon côté. Je n'aurai pas peur. Que peut me faire l'homme?
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
7 Yahvé est de mon côté parmi ceux qui m'aident. C'est pourquoi je regarderai avec triomphe ceux qui me haïssent.
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
8 Il vaut mieux se réfugier en Yahvé, que de faire confiance à l'homme.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
9 Il vaut mieux se réfugier en Yahvé, que de faire confiance aux princes.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
10 Toutes les nations m'ont entouré, mais au nom de Yahvé, je les ai éliminés.
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
11 Ils m'ont entouré, oui, ils m'ont entouré. Au nom de Yahvé, je les ai en effet éliminés.
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
12 Ils m'ont entouré comme des abeilles. Ils sont éteints comme les épines brûlantes. Au nom de Yahvé, je les ai éliminés.
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
13 Tu m'as poussé fort en arrière, pour me faire tomber, mais Yahvé m'a aidé.
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
14 L'Éternel est ma force et mon chant. Il est devenu mon salut.
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
15 La voix de l'allégresse et du salut est dans les tentes des justes. « La main droite de Yahvé agit avec courage.
Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
16 La droite de Yahvé est exaltée! La main droite de Yahvé est vaillante! »
An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
17 Je ne veux pas mourir, mais vivre, et déclarer les œuvres de Yah.
Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
18 L'Éternel m'a sévèrement puni, mais il ne m'a pas livré à la mort.
Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
19 Ouvrez-moi les portes de la justice. Je vais entrer en eux. Je vais rendre grâce à Yah.
Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
20 Voici la porte de l'Éternel; les justes y entreront.
Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
21 Je te rendrai grâce, car tu m'as exaucé, et sont devenus mon salut.
Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
22 La pierre que les bâtisseurs ont rejetée est devenu la pierre angulaire.
Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
23 C'est l'œuvre de Yahvé. C'est merveilleux à nos yeux.
Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
24 Voici le jour que Yahvé a établi. Nous nous en réjouirons et en serons heureux!
Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
25 Sauve-nous maintenant, nous t'en supplions, Yahvé! Yahvé, nous t'en supplions, envoie la prospérité maintenant.
Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
26 Béni soit celui qui vient au nom de Yahvé! Nous vous avons béni de la maison de Yahvé.
Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
27 Yahvé est Dieu, et il nous a donné la lumière. Liez le sacrifice avec des cordes, jusqu'aux cornes de l'autel.
Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
28 Tu es mon Dieu, et je te rendrai grâce. Tu es mon Dieu, je t'exalte.
Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
29 Oh! Rendez grâce à Yahvé, car il est bon, car sa bonté est éternelle.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.

< Psaumes 118 >