< Psaumes 11 >

1 Pour le musicien en chef. Par David. En Yahvé, je me réfugie. Comment peux-tu dire à mon âme: « Fuis comme un oiseau vers ta montagne »?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
2 Car voici, les méchants bandent leurs arcs. Ils ont placé leurs flèches sur les cordes, pour qu'ils puissent tirer dans l'obscurité sur ceux qui ont le cœur droit.
Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
3 Si les fondations sont détruites, que peut faire le juste?
Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
4 Yahvé est dans son temple saint. Yahvé est sur son trône dans le ciel. Ses yeux observent. Ses yeux examinent les enfants des hommes.
Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
5 Yahvé examine les justes, mais son âme déteste le méchant et celui qui aime la violence.
Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
6 Sur les méchants, il fait pleuvoir des charbons ardents; le feu, le soufre et le vent brûlant seront la part de leur coupe.
A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
7 Car Yahvé est juste. Il aime la droiture. Les hommes droits verront sa face.
Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.

< Psaumes 11 >