< Psaumes 106 >

1 Louez Yahvé! Rendez grâce à Yahvé, car il est bon, car sa bonté est éternelle.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Qui peut dire les actes puissants de Yahvé, ou de déclarer pleinement toutes ses louanges?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Heureux ceux qui gardent la justice. Heureux celui qui fait ce qui est juste à tout moment.
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Souviens-toi de moi, Yahvé, avec la faveur que tu témoignes à ton peuple. Rendez-moi visite avec votre salut,
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 afin que je voie la prospérité de tes élus, afin que je me réjouisse de l'allégresse de ta nation, afin que je puisse me glorifier avec votre héritage.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Nous avons péché avec nos pères. Nous avons commis une iniquité. Nous avons fait le mal.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Nos pères n'ont pas compris tes merveilles en Égypte. Ils ne se sont pas souvenus de la multitude de tes bontés, mais se sont rebellés à la mer, même à la mer Rouge.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Mais il les a sauvés à cause de son nom, pour faire connaître sa puissance.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 Il menaça aussi la mer Rouge, et elle fut mise à sec; Il les a donc conduits dans les profondeurs, comme dans un désert.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 Il les a sauvés de la main de celui qui les haïssait, et les a rachetés de la main de l'ennemi.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 Les eaux ont recouvert leurs adversaires. Il n'y en avait plus un seul.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Et ils crurent à ses paroles. Ils ont chanté ses louanges.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Ils ont vite oublié ses œuvres. Ils n'ont pas attendu son conseil,
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 mais a cédé à la soif dans le désert, et ont testé Dieu dans le désert.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Il leur accorda leur demande, mais a envoyé la maigreur dans leur âme.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 Ils enviaient aussi Moïse dans le camp, et Aaron, le saint de Yahvé.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 La terre s'ouvrit et engloutit Dathan, et a couvert la compagnie d'Abiram.
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 Un feu s'est allumé en leur compagnie. La flamme a brûlé les méchants.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Ils firent un veau à Horeb, et ont adoré une image en fusion.
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 Ils ont ainsi échangé leur gloire pour une image d'un taureau qui mange de l'herbe.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 Ils ont oublié Dieu, leur Sauveur, qui avait fait de grandes choses en Égypte,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 merveilles dans le pays de Ham, et des choses impressionnantes près de la Mer Rouge.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 C'est pourquoi il a dit qu'il allait les détruire, si Moïse, son élu, ne s'était pas tenu devant lui sur la brèche, pour détourner sa colère, afin qu'il ne les détruise pas.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Oui, ils ont méprisé la terre agréable. Ils n'ont pas cru sa parole,
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 mais ils murmuraient dans leurs tentes, et n'ont pas écouté la voix de Yahvé.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Il leur a donc juré qu'il les renverserait dans le désert,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 qu'il anéantirait leur descendance parmi les nations, et les disperser dans les pays.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 Ils s'attachèrent aussi à Baal Peor, et ont mangé les sacrifices des morts.
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Ils l'ont ainsi irrité par leurs actes. La peste s'est abattue sur eux.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Alors Phinées se leva et exécuta le jugement, ainsi la peste a été arrêtée.
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 Cela lui a été crédité comme justice, pour toutes les générations à venir.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 Ils l'ont aussi irrité aux eaux de Meriba, de sorte que Moïse a été troublé à cause d'eux;
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 parce qu'ils étaient rebelles à son esprit, il a parlé sans réfléchir avec ses lèvres.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 Ils n'ont pas détruit les peuples, comme Yahvé le leur a ordonné,
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 mais se sont mêlés aux nations, et appris leurs œuvres.
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 Ils ont servi leurs idoles, qui est devenu un piège pour eux.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Oui, ils ont sacrifié leurs fils et leurs filles aux démons.
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 Ils ont versé du sang innocent, même le sang de leurs fils et de leurs filles, qu'ils ont sacrifié aux idoles de Canaan. La terre était polluée par le sang.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Ils se sont ainsi souillés par leurs œuvres, et se prostituaient dans leurs actes.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 C'est pourquoi Yahvé s'est enflammé de colère contre son peuple. Il abhorrait son héritage.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 Il les a livrés aux mains des nations. Ceux qui les détestaient les dominaient.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Leurs ennemis les ont aussi opprimés. Ils ont été soumis à leur autorité.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Il les a secourus à plusieurs reprises, mais ils ont été rebelles dans leurs conseils, et ont été abaissés dans leur iniquité.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Mais il a considéré leur détresse, quand il a entendu leur cri.
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 Il s'est souvenu pour eux de son alliance, et se sont repentis selon la multitude de ses bontés.
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 Il a fait en sorte qu'ils soient aussi à plaindre. par tous ceux qui les ont emmenés en captivité.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Sauve-nous, Yahvé, notre Dieu, nous rassembler d'entre les nations, pour rendre grâce à ton saint nom, pour triompher dans ta louange!
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Béni soit Yahvé, le Dieu d'Israël, de l'éternité à l'éternité! Que tout le monde dise: « Amen. » Louez Yah!
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< Psaumes 106 >