< Psaumes 102 >
1 Prière de l'affligé, lorsqu'il est accablé et qu'il déverse sa plainte devant Yahvé. Entends ma prière, Yahvé! Laisse mon cri venir à toi.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Ne me cache pas ta face au jour de ma détresse. Tourne ton oreille vers moi. Répondez rapidement dans la journée lorsque j'appelle.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Car mes jours se consument comme de la fumée. Mes os sont brûlés comme une torche.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Mon cœur est flétri comme l'herbe, il est desséché, car j'oublie de manger mon pain.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 A cause de la voix de mes gémissements, mes os collent à ma peau.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Je suis comme un pélican du désert. Je suis devenu comme un hibou des lieux déserts.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Je veille, et je suis devenu comme un moineau qui est seul sur le toit.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Mes ennemis m'outragent tout le jour. Ceux qui sont en colère contre moi utilisent mon nom comme une malédiction.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Car j'ai mangé de la cendre comme du pain, et j'ai mélangé ma boisson avec des larmes,
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 à cause de ton indignation et de ta colère; car tu m'as pris et jeté au loin.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Mes jours sont comme une longue ombre. Je me suis flétri comme l'herbe.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 Mais toi, Yahvé, tu demeures à jamais; ta renommée perdure à travers les générations.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Tu te lèveras et tu auras pitié de Sion, car il est temps d'avoir pitié d'elle. Oui, le moment est venu.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Car tes serviteurs prennent plaisir à ses pierres, et ayez pitié de sa poussière.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Ainsi les nations craindront le nom de Yahvé, tous les rois de la terre, ta gloire.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 Car Yahvé a rebâti Sion. Il est apparu dans sa gloire.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 Il a répondu à la prière des indigents, et n'a pas méprisé leur prière.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Ceci sera écrit pour la génération à venir. Un peuple qui sera créé louera Yah,
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 car il a regardé du haut de son sanctuaire. Du ciel, Yahvé a vu la terre,
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 pour entendre les gémissements du prisonnier, pour libérer ceux qui sont condamnés à mort,
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 afin que les hommes proclament le nom de Yahvé dans Sion, et ses louanges à Jérusalem,
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 quand les peuples seront rassemblés, les royaumes, pour servir Yahvé.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Il a affaibli ma force le long du parcours. Il a raccourci mes jours.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 J'ai dit: « Mon Dieu, ne m'enlève pas au milieu de mes jours. Vos années sont à travers toutes les générations.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Dès longtemps, tu as posé les fondements de la terre. Les cieux sont l'œuvre de tes mains.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Ils périront, mais toi tu persévéreras. Oui, ils s'useront tous comme un vêtement. Tu les changeras comme un manteau, et ils seront changés.
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 Mais vous êtes les mêmes. Vos années n'auront pas de fin.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Les enfants de tes serviteurs continueront. Leur progéniture sera établie devant toi. »
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”