< Psaumes 101 >
1 Un psaume de David. Je chanterai la bonté et la justice. A toi, Yahvé, je chanterai des louanges.
Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
2 Je veillerai à mener une vie irréprochable. Quand viendras-tu me voir? Je marcherai dans ma maison avec un cœur irréprochable.
Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
3 Je ne mettrai pas de choses viles devant mes yeux. Je déteste les actes des hommes sans foi. Ils ne s'accrocheront pas à moi.
Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
4 Un cœur pervers sera loin de moi. Je ne veux rien avoir à faire avec le mal.
Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
5 Je ferai taire celui qui calomnie secrètement son prochain. Je ne tolérerai pas celui qui est arrogant et prétentieux.
Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
6 Mes yeux se porteront sur les fidèles du pays, pour qu'ils puissent habiter avec moi. Celui qui marche d'une manière parfaite, il me servira.
Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
7 Celui qui pratique la tromperie n'habitera pas dans ma maison. Celui qui dit des mensonges ne sera pas établi devant mes yeux.
Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
8 Matin après matin, je détruirai tous les méchants du pays, pour exterminer de la cité de Yahvé tous les artisans de l'iniquité.
Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.