< Psaumes 10 >

1 Pourquoi te tiens-tu à l'écart, Yahvé? Pourquoi vous cachez-vous dans les moments difficiles?
Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
2 Dans leur arrogance, les méchants traquent les faibles. Ils sont pris dans les combines qu'ils conçoivent.
Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
3 Car le méchant se vante des désirs de son cœur. Il bénit les cupides et condamne Yahvé.
Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
4 Le méchant, dans l'orgueil de son visage, n'a pas de place dans ses pensées pour Dieu.
Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
5 Ses voies sont prospères en tout temps. Il est arrogant, et vos lois sont loin de sa vue. Quant à tous ses adversaires, il se moque d'eux.
Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
6 Il dit en son cœur: « Je ne serai pas ébranlé. Pour les générations à venir, je n'aurai aucun problème. »
Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
7 Sa bouche est pleine de malédiction, de tromperie et d'oppression. Sous sa langue se cachent la malice et l'iniquité.
Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
8 Il se tient à l'affût près des villages. Depuis des embuscades, il assassine les innocents. Ses yeux sont secrètement tournés vers les personnes sans défense.
Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
9 Il se tapit en secret comme un lion dans son embuscade. Il est à l'affût pour attraper les impuissants. Il attrape les impuissants quand il les prend dans son filet.
Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
10 Les impuissants sont écrasés. Ils s'effondrent. Ils tombent sous sa coupe.
Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
11 Il dit dans son cœur: « Dieu a oublié. Il cache son visage. Il ne le verra jamais. »
Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
12 Lève-toi, Yahvé! Dieu, lève ta main! N'oubliez pas les impuissants.
Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
13 Pourquoi le méchant condamne-t-il Dieu, et dire dans son cœur, « Dieu ne me demandera pas de comptes »?
Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
14 Mais vous voyez la détresse et le chagrin. Vous le considérez pour le prendre en main. Vous aidez la victime et l'orphelin.
Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
15 Brisez le bras des méchants. Quant à l'homme mauvais, cherche sa méchanceté jusqu'à ce que tu n'en trouves aucune.
Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
16 Yahvé est roi pour les siècles des siècles! Les nations périront hors de son pays.
Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
17 Yahvé, tu as entendu le désir des humbles. Vous allez préparer leur cœur. Tu feras en sorte que ton oreille entende,
Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
18 pour juger l'orphelin et l'opprimé, pour que l'homme qui est de la terre ne soit plus terrifié.
kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.

< Psaumes 10 >