< Proverbes 7 >
1 Mon fils, garde mes paroles. Portez mes commandements en vous.
Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
2 Observez mes commandements et vivez! Garde mon enseignement comme la prunelle de tes yeux.
Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
3 Liez-les sur vos doigts. Écris-les sur la tablette de ton cœur.
Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Dis à la sagesse: « Tu es ma sœur. » Appelez la compréhension de votre parent,
Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
5 afin qu'ils te préservent de la femme étrangère, de l'étrangère qui flatte avec ses mots.
za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
6 Car à la fenêtre de ma maison, J'ai regardé à travers mon treillis.
A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
7 J'ai vu parmi les simples. J'ai discerné parmi les jeunes un jeune homme dépourvu d'intelligence,
Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
8 passant dans la rue près de son coin, il a pris le chemin de sa maison,
Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
9 au crépuscule, au soir du jour, au milieu de la nuit et dans l'obscurité.
da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
10 Voici qu'une femme vint à sa rencontre, vêtue comme une prostituée, et avec une intention maligne.
Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
11 Elle est bruyante et provocante. Ses pieds ne restent pas dans sa maison.
(Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
12 Maintenant elle est dans les rues, maintenant sur les places, et se cachant à chaque coin de rue.
wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
13 Alors elle le saisit et l'embrassa. Avec un visage impudent, elle lui dit:
Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
14 « Les sacrifices d'actions de grâces sont avec moi. Aujourd'hui, je me suis acquitté de mes vœux.
“Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
15 C'est pourquoi je suis sorti à ta rencontre, pour chercher assidûment ta face, et je t'ai trouvé.
Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
16 J'ai étendu ma couche avec des tapis de tapisserie, avec des tissus rayés de la laine d'Égypte.
Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
17 J'ai parfumé mon lit avec de la myrrhe, de l'aloès et de la cannelle.
Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
18 Venez, prenons notre dose d'amour jusqu'au matin. Consolons-nous en aimant.
Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
19 Car mon mari n'est pas à la maison. Il est parti pour un long voyage.
Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
20 Il a pris avec lui un sac d'argent. Il reviendra à la maison à la pleine lune. »
Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
21 Avec des paroles persuasives, elle l'a égaré. Avec la flatterie de ses lèvres, elle l'a séduit.
Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
22 Il la suivit immédiatement, comme un bœuf va à l'abattoir, comme un idiot qui se prend les pieds dans un nœud coulant.
Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
23 Jusqu'à ce qu'une flèche lui transperce le foie, comme un oiseau qui se précipite vers le piège, et ne sait pas que ça va lui coûter la vie.
sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
24 Maintenant donc, mes fils, écoutez-moi. Faites attention aux mots de ma bouche.
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
25 Ne laisse pas ton cœur se tourner vers ses voies. Ne vous égarez pas dans ses sentiers,
Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
26 car elle a jeté de nombreux blessés. Oui, tous ses morts sont une puissante armée.
Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
27 Sa maison est le chemin du séjour des morts, en descendant dans les chambres de la mort. (Sheol )
Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol )