< Nombres 36 >

1 Les chefs de famille des fils de Galaad, fils de Makir, fils de Manassé, des familles des fils de Joseph, s'approchèrent et parlèrent devant Moïse et devant les princes, les chefs de famille des enfants d'Israël.
Sai shugabannin gidajen iyalan Gileyad ɗan Makir, ɗan Manasse, waɗanda suka fito daga kabilar zuriyar Yusuf, suka zo, suka yi magana a gaban Musa da shugabanni, shugabannin iyalan Isra’ilawa.
2 Ils dirent: « Yahvé a ordonné à mon seigneur de donner le pays en héritage par tirage au sort aux enfants d'Israël. Mon seigneur a reçu l'ordre de Yahvé de donner l'héritage de Zelophehad, notre frère, à ses filles.
Suka ce, “Sa’ad da Ubangiji ya umarce ranka yă daɗe, yă raba ƙasar gādo ga Isra’ilawa ta wurin ƙuri’a, ya umarce ka, ka ba wa’ya’ya matan nan na Zelofehad ɗan’uwanmu gādonsa.
3 Si elles se marient à l'un des fils des autres tribus des enfants d'Israël, leur héritage sera retranché de l'héritage de nos pères et ajouté à l'héritage de la tribu à laquelle elles appartiendront. Il sera ainsi retranché du lot de notre héritage.
To, a ce sun auri mutane daga waɗansu kabilan Isra’ilawa fa; ka ga, za a ɗebe gādonsu daga gādon kakanninmu a ƙara wa gādon kabilan mutanen da suka aura ke nan. Ta haka za a ɗebe sashe daga gādon da aka ba mu ke nan.
4 Quand viendra le jubilé des enfants d'Israël, leur héritage sera ajouté à l'héritage de la tribu à laquelle ils appartiendront. Ainsi leur héritage sera retranché de l'héritage de la tribu de nos pères. »
Sa’ad da Shekara ta Murnar Isra’ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, a kuma ba su mallakar gādon da aka ɗebe daga kabilar kakanninmu.”
5 Moïse donna aux enfants d'Israël un ordre conforme à la parole de Yahvé, en disant: « La tribu des fils de Joseph dit ce qui est juste.
Ta wurin umarnin Ubangiji, Musa ya ba Isra’ilawa wannan umarni, “Abin da kabilar zuriyar Yusuf suke faɗi, daidai ne.
6 Voici ce que l'Éternel ordonne pour les filles de Zelophehad: Qu'elles se marient à qui bon leur semble, mais elles se marieront dans la famille de la tribu de leur père.
Ga abin da Ubangiji ya umarta saboda’ya’ya matan nan na Zelofehad. Za su iya auri duk wanda suka ga dama, muddin sun yi aure a cikin kabilar kakanninsu.
7 Ainsi, aucun héritage des enfants d'Israël ne passera d'une tribu à l'autre, car les enfants d'Israël conserveront tous l'héritage de la tribu de leurs pères.
Ba gādon Isra’ilan da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowane mutumin Isra’ila zai riƙe gādonsa na kabilar da ya gāda daga kakanninsa.
8 Toute fille qui possédera un héritage dans une tribu des enfants d'Israël sera la femme d'un membre de la famille de la tribu de son père, afin que les enfants d'Israël possèdent chacun l'héritage de leurs pères.
Kowace’ya wadda ta ci gādon ƙasa, a kowace kabilar Isra’ilawa, dole tă auri wani cikin kabilar kakanninta, saboda kowane mutumin Isra’ila yă mallaki gādon kakanninsa.
9 Ainsi, aucun héritage ne passera d'une tribu à une autre tribu, car les tribus des enfants d'Israël garderont chacune leur héritage.'"
Ba gādon da za a ba wa wata kabila daga wata kabila, gama kowace kabilar Isra’ilawa za tă riƙe mallaka da ta gāda.”
10 Les filles de Tselophehad firent ce que l'Éternel avait ordonné à Moïse:
Saboda haka’ya’yan Zelofehad mata suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
11 car Mahla, Tirza, Hogla, Milca et Noé, filles de Tselophehad, furent mariées aux fils des frères de leur père.
’Ya’yan Zelofehad mata, Mala, Tirza, Hogla, Milka da Nowa, suka auri’ya’yan’yan’uwa na gefen mahaifinsu.
12 Elles furent mariées dans les familles des fils de Manassé, fils de Joseph. Leur héritage resta dans la tribu de la famille de leur père.
Suka yi aure cikin kabilar zuriyar Manasse ɗan Yusuf, gādonsu kuwa ya kasance a cikin iyali da kuma kabilar mahaifinsu.
13 Tels sont les commandements et les ordonnances que Yahvé a prescrits par Moïse aux enfants d'Israël dans les plaines de Moab, près du Jourdain, à Jéricho.
Waɗannan su ne umarnai da ƙa’idodin da Ubangiji ya ba wa Isra’ilawa ta wurin Musa, a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.

< Nombres 36 >