< Nombres 34 >

1 L'Éternel parla à Moïse, et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Donne cet ordre aux enfants d`Israël, et dis-leur: Lorsque vous entrerez dans le pays de Canaan, le pays qui vous sera donné en héritage, le pays de Canaan, selon ses limites,
“Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
3 votre quart méridional partira du désert de Tsin, le long du côté d`Édom, et votre limite méridionale partira de l`extrémité de la mer Salée, à l`orient.
“‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
4 Votre frontière tournera au sud de la montée d'Akrabbim, et passera à Tsin; elle passera au sud de Kadès Barnea; de là, elle ira à Hazar Addar, et passera à Azmon.
tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
5 La frontière tournera depuis Azmon vers le ruisseau d'Égypte, et s'arrêtera à la mer.
inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
6 "'Pour la frontière occidentale, tu auras la grande mer et son bord. Ce sera ta frontière occidentale.
“‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
7 « Voici quelle sera votre limite septentrionale: depuis la grande mer, vous tracerez pour vous la montagne de Hor.
“‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
8 De la montagne de Hor, vous marquerez l'entrée de Hamath, et la frontière passera par Zedad.
za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
9 Puis la frontière ira jusqu'à Ziphron, et se terminera à Hazar Enan. Ce sera votre frontière nord.
tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
10 Tu délimiteras ta frontière orientale de Hazar Enan à Shepham.
“‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
11 La frontière descendra de Shepham à Riblah, à l'est d'Ain. La limite descendra et s'étendra jusqu'au bord de la mer de Chinnereth, à l'est.
Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
12 La frontière descendra jusqu'au Jourdain et se terminera à la mer Salée. Tel sera votre pays, selon les frontières qui l'entourent. »
Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
13 Moïse donna cet ordre aux enfants d'Israël: Voici le pays dont vous hériterez par le sort, et que l'Éternel a ordonné de donner aux neuf tribus et à la demi-tribu.
Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
14 La tribu des fils de Ruben, selon les maisons de leurs pères, la tribu des fils de Gad, selon les maisons de leurs pères, et la demi-tribu de Manassé, ont reçu leur héritage.
saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
15 Les deux tribus et la demi-tribu ont reçu leur héritage au-delà du Jourdain, à Jéricho, à l'est, vers le soleil levant. »
Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
16 Yahvé parla à Moïse, et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Voici les noms des hommes qui vous partageront le pays en héritage: Le prêtre Éléazar et Josué, fils de Nun.
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18 Tu prendras un prince de chaque tribu, pour partager le pays en héritage.
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19 Voici les noms de ces hommes: Pour la tribu de Juda: Caleb, fils de Jephunné.
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20 Pour la tribu des fils de Siméon: Shemuel, fils d'Ammihud.
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21 pour la tribu de Benjamin: Elidad, fils de Chislon
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22 pour la tribu des fils de Dan: un prince, Bukki, fils de Jogli
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23 Pour les fils de Joseph: de la tribu des fils de Manassé, le prince Hanniel, fils d'Ephod.
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24 pour la tribu des fils d'Éphraïm: le prince Kemuel, fils de Shiphtan
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25 pour la tribu des fils de Zabulon: le prince Elizaphan, fils de Parnach
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26 pour la tribu des fils d'Issacar, le prince Paltiel, fils d'Azzan.
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27 pour la tribu des fils d'Aser, le prince Ahihud, fils de Shelomi
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28 pour la tribu des fils de Nephthali, le prince Pedahel, fils d'Ammihud ».
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29 Tels sont ceux à qui Yahvé ordonna de faire le partage de l'héritage des enfants d'Israël dans le pays de Canaan.
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.

< Nombres 34 >