< Nombres 24 >

1 Lorsque Balaam vit qu'il plaisait à Yahvé de bénir Israël, il n'alla pas, comme les autres fois, recourir à la divination, mais il tourna son visage vers le désert.
To, da Bala’am ya ga cewa Ubangiji yana jin daɗin sa wa Isra’ila albarka, bai koma wajen sihiri kamar dā ba, amma ya juya fuskarsa wajen hamada.
2 Balaam leva les yeux, et il vit Israël habitant selon ses tribus; et l'Esprit de Dieu vint sur lui.
Da Bala’am ya duba sai ya ga Isra’ila sun yi sansani kabila, kabila, Ruhun Allah kuwa ya sauko masa,
3 Il reprit sa parabole, et dit, « Balaam, fils de Beor, dit, l'homme dont les yeux sont ouverts dit;
sai ya yi annabcinsa ya ce, “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
4 dit-il, qui entend les paroles de Dieu, qui voit la vision du Tout-Puissant, en tombant, et en ayant les yeux ouverts:
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, maganar wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, mutumin da ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
5 Que tes tentes sont belles, Jacob! et tes habitations, Israël!
“Ina misalin kyan tentunanka, ya Yaƙub, wuraren zamanka, ya Isra’ila!
6 Ils s'étendent comme des vallées, comme des jardins au bord de la rivière, comme des aloès que Yahvé a plantés, comme des cèdres au bord de l'eau.
“Kamar kwaruruka suke a shimfiɗe, kamar lambu kusa da rafi, kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa, kamar itatuwa al’ul kusa da ruwaye.
7 L'eau coulera de ses seaux. Sa semence sera dans de nombreuses eaux. Son roi sera plus haut qu'Agag. Son royaume sera exalté.
Ruwa zai kwararo daga bokitinsu; irinsu za su sami ruwa a yalwace. “Sarkinsu zai fi sarkin Agag; mulkinsu zai ɗaukaka.
8 Dieu le fait sortir d'Égypte. Il a pour ainsi dire la force du bœuf sauvage. Il consumera les nations, ses adversaires, brisera leurs os en morceaux, et les transpercer de ses flèches.
“Allah ya fitar da su daga Masar; suna da ƙarfin kutunkun ɓauna. Sun cinye abokan gāban, suka kakkarya ƙasusuwansu; da kibiyoyinsu suka sossoke su.
9 Il s'est couché, il s'est couché comme un lion, comme une lionne; qui le réveillera? Tous ceux qui vous bénissent sont bénis. Tous ceux qui te maudissent sont maudits. »
Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”
10 La colère de Balak s'enflamma contre Balaam, et il frappa ses mains l'une contre l'autre. Balak dit à Balaam: « Je t'ai appelé pour que tu maudisses mes ennemis, et voici que tu les as tous bénis ces trois fois.
Fushin Balak ya ƙuna a kan Bala’am. Ya tafa hannunsa, ya ce masa, “Na kira ka don ka la’anta abokan gābana, amma sai ga shi ka sa musu albarka har sau uku.
11 C'est pourquoi, fuis à ta place, maintenant! Je pensais te promouvoir à de grands honneurs, mais voici que Yahvé t'en a empêché. »
Yanzu ka bar nan ka tafi gida! Na ce zan sāka maka da lada mai kyau, amma Ubangiji ya hana ka samun ladan.”
12 Balaam dit à Balak: « N'ai-je pas dit à tes messagers que tu m'as envoyés:
Bala’am ya ce wa Balak, “Ban faɗa wa’yan aikan da ka aiko wurina ba cewa,
13 « Si Balak me donne sa maison pleine d'argent et d'or, je ne peux pas aller au-delà de la parole de Yahvé, pour faire du bien ou du mal de mon propre chef. Je dirai ce que dit l'Éternel »?
‘Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba, kuma dole in faɗa abin da Ubangiji ya ce ne kawai’?
14 Maintenant, voici que je vais vers mon peuple. Viens, je vais t'informer de ce que ce peuple fera à ton peuple dans la suite des temps. »
Yanzu zan koma wajen mutanena, amma bari in gargaɗe ka game da abin da mutanen nan za su yi wa mutanenka cikin kwanaki masu zuwa.”
15 Il reprit sa parabole, et dit, « Balaam, fils de Beor, dit, l'homme dont les yeux sont ouverts dit;
Sa’an nan ya furta saƙonsa. “Maganar Bala’am ɗan Beyor, saƙon mutumin da idanunsa ke gani sarai,
16 il dit, qui entend les paroles de Dieu, connaît la connaissance du Très-Haut, et qui voit la vision du Tout-Puissant, en tombant, et en ayant les yeux ouverts:
maganar mutumin da ya saurari maganar Allah, wanda yake da sani daga Mafi Ɗaukaka, wanda yake ganin wahayi daga Maɗaukaki, wanda ya fāɗi rubda ciki, wanda kuma idanunsa suna a buɗe.
17 Je le vois, mais pas maintenant. Je le vois, mais pas près. Une étoile sortira de Jacob. Un sceptre s'élèvera d'Israël, et il frappera les coins de Moab, et écraser tous les fils de Sheth.
“Na gan shi, amma ba yanzu ba; na hange shi, amma ba kusa ba. Tauraro zai fito daga Yaƙub; sandan mulki zai fito daga Isra’ila. Zai ragargaje goshin Mowab, kawunan dukan’ya’yan Set.
18 Edom sera une possession. Séir, son ennemi, sera aussi une possession, alors qu'Israël le fait vaillamment.
Za a ci Edom da yaƙi; za a ci Seyir, abokiyar gābanta, amma Isra’ila zai ƙara ƙarfi.
19 De Jacob, un seul dominera, et détruira le reste de la ville. »
Mai mulki zai fito daga Yaƙub yă hallaka waɗanda suka ragu a birnin.”
20 Il regarda Amalek, et reprit sa parabole, et dit, « Amalek était la première des nations, mais sa finalité sera la destruction. »
Sai Bala’am ya ga Amalek, ya kuma furta maganarsa. “Amalek yana cikin al’ummai na fari, amma zai zama na ƙarshen da za a hallaka.”
21 Il regarda le Kenite, et reprit sa parabole, et dit, « Ta demeure est forte. Votre nid est fixé dans la roche.
Sai ya ga Keniyawa, ya kuma furta maganarsa. “Wurin zamanku lafiya yake, an kuma sa sheƙarku a cikin duwatsu;
22 Cependant, Kain sera perdue, jusqu'à ce qu'Asshur vous emmène en captivité. »
duk da haka, za a hallaka ku Keniyawa sa’ad da Asshur ya kame ku.”
23 Il reprit sa parabole, et dit, « Hélas, qui vivra quand Dieu fera cela?
Sai ya furta maganarsa ya ce, “Wayyo, wa zai rayu sa’ad da Allah ya yi haka?
24 Mais des navires viendront de la côte de Kittim. Ils feront souffrir Asshur, et ils feront souffrir Eber. Lui aussi viendra à la destruction. »
Jiragen ruwa za su zo daga Kittim; za su murƙushe Asshur da Eber, amma su ma za a hallaka su.”
25 Balaam se leva, et s'en alla et retourna à sa place; et Balak aussi s'en alla.
Sa’an nan Bala’am ya tashi ya koma gidan, Balak kuma ya yi tafiyarsa.

< Nombres 24 >