< Néhémie 1 >
1 Paroles de Néhémie, fils de Hacalia. Au mois de Chislev de la vingtième année, comme je me trouvais dans le palais de Suse,
Kalmomin Nehemiya ɗan Hakaliya. A cikin watan Kisleb a shekara ta ashirin, yayinda nake a fadar Shusha.
2 Hanani, l'un de mes frères, arriva, lui et quelques hommes de Juda, et je les interrogeai sur les Juifs qui s'étaient échappés, sur ceux qui restaient de la captivité, et sur Jérusalem.
Hanani, ɗaya daga cikin’yan’uwana, ya zo daga Yahuda tare da waɗansu mutane. Na kuwa tambaye shi game da raguwar Yahudawan da suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta, da kuma game da Urushalima.
3 Ils me répondirent: « Les restes de la captivité qui sont restés dans la province sont dans une grande détresse et dans l'opprobre. La muraille de Jérusalem est aussi détruite, et ses portes sont brûlées par le feu. »
Suka ce mini, “Waɗanda suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta da kuma suka komo cikin yankin suna cikin babban damuwa da wulaƙanci. An rushe katangar Urushalima aka kuma ƙone ƙofofin da wuta.”
4 Lorsque j'entendis ces paroles, je m'assis et je pleurai, et je fus en deuil pendant plusieurs jours; Je jeûnai et je priai devant le Dieu des cieux,
Da na ji waɗannan abubuwa, sai na zauna na yi kuka. Na yi kwanaki ina makoki da azumi, na kuma yi addu’a a gaban Allah na sama.
5 et je dis: « Je t'en supplie, Yahvé, le Dieu des cieux, le Dieu grand et redoutable qui garde l'alliance et la bonté envers ceux qui l'aiment et qui gardent ses commandements,
Na ce, “Ya Ubangiji Allah na sama, Allah mai girma da mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna da waɗanda suke ƙaunarsa, suke kuma yin biyayya da umarnansa,
6 que ton oreille soit attentive et tes yeux ouverts, afin que tu puisses écouter la prière de ton serviteur que je fais devant toi en ce moment, jour et nuit, pour les enfants d'Israël, tes serviteurs, tandis que je confesse les péchés des enfants d'Israël que nous avons commis contre toi. Oui, moi et la maison de mon père avons péché.
ka sa kunne ka kuma buɗe idanunka ka ji addu’ar da bawanka yake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra’ila. Na furta zunuban da mu Isra’ilawa, har da ni da kuma gidan mahaifina muka yi maka.
7 Nous nous sommes montrés très corrompus envers toi, et nous n'avons pas observé les commandements, les lois et les ordonnances que tu avais prescrits à ton serviteur Moïse.
Mun yi mugunta gare ka. Ba mu yi biyayya da umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da ka ba wa bawanka Musa ba.
8 « Souviens-toi, je t'en prie, de la parole que tu as donnée à Moïse, ton serviteur, en disant: « Si vous commettez une infidélité, je vous disperserai parmi les peuples;
“Ka tuna da umarnan da ka ba wa bawanka Musa, kana cewa, ‘In kun yi rashin aminci, zan warwatsar da ku a cikin al’ummai,
9 mais si vous revenez à moi, si vous gardez mes commandements et si vous les mettez en pratique, quand vos exilés seraient à l'extrémité des cieux, je les rassemblerai de là et je les amènerai dans le lieu que j'ai choisi, pour y faire résider mon nom ».
amma in kuka dawo gare ni kuka kuma yi biyayya da umarnaina, to, ko mutanenku da aka kwasa zuwa zaman bauta suna can wuri mafi nisa, zan tattara su daga can in kawo su wurin da na zaɓa yă zama wurin zama don Sunana.’
10 « Voici tes serviteurs et ton peuple, que tu as rachetés par ta grande puissance et par ta main forte.
“Su bayinka ne da kuma mutanenka da ka fansa ta wurin ƙarfinka mai girma da kuma hannunka mai iko.
11 Seigneur, je t'en prie, que ton oreille soit maintenant attentive à la prière de ton serviteur, et à la prière de tes serviteurs qui aiment à craindre ton nom; fais prospérer aujourd'hui ton serviteur, et accorde-lui la miséricorde aux yeux de cet homme. » J'étais le porteur de coupe du roi.
Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu’ar wannan bawanka da kuma ga addu’ar bayinka waɗanda suke farin cikin girmama sunanka. Ka ba wa bawanka nasara a yau ta wurinsa yă sami tagomashi a gaban wannan mutum.” Ni ne mai riƙon kwaf sarki.