< Néhémie 6 >

1 Lorsqu'on eut appris à Sanballat, à Tobija, à Guéshem l'Arabe et au reste de nos ennemis que j'avais construit la muraille et qu'il n'y avait plus de brèche, bien que je n'eusse pas encore posé les battants des portes,
Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
2 Sanballat et Guéshem m'envoyèrent dire: « Viens, rencontrons-nous dans les villages de la plaine d'Ono. Rencontrons-nous ensemble dans les villages de la plaine d'Ono. » Mais ils avaient l'intention de me faire du mal.
Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
3 J'ai envoyé des messagers vers eux, en disant: « Je fais une grande œuvre, de sorte que je ne peux pas descendre. Pourquoi l'œuvre cesserait-elle alors que je la quitte pour descendre vers vous? »
saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
4 Ils m'envoyèrent quatre fois de la sorte, et je leur répondis de la même manière.
Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
5 Alors Sanballat m'envoya son serviteur de la même manière, la cinquième fois, avec une lettre ouverte à la main,
Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
6 dans laquelle était écrit: « On raconte parmi les nations, et Gashmu le dit, que toi et les Juifs avez l'intention de vous rebeller. C'est pour cela que vous construisez le mur. Tu serais leur roi, selon ces paroles.
wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
7 Tu as aussi désigné des prophètes pour annoncer ta venue à Jérusalem, en disant: « Il y a un roi en Juda! ». Maintenant, on le rapportera au roi selon ces paroles. Viens donc maintenant, et tenons conseil ensemble. »
har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
8 Alors je lui envoyai dire: « Ce n'est pas ce que tu dis qui se fait, mais tu l'imagines de ton propre cœur. »
Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
9 Car tous auraient voulu nous effrayer, en disant: « Leurs mains seront affaiblies par l'œuvre, et elle ne se fera pas. » Mais maintenant, fortifie mes mains.
Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
10 Je me rendis à la maison de Shemahia, fils de Delaia, fils de Méhétabel, qui était enfermé chez lui, et il dit: « Réunissons-nous dans la maison de Dieu, à l'intérieur du temple, et fermons les portes du temple, car ils viendront te tuer. Oui, dans la nuit, ils viendront pour te tuer. »
Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
11 J'ai dit: « Un homme comme moi doit-il fuir? Qui est là qui, étant tel que moi, irait dans le temple pour sauver sa vie? Je n'y entrerai pas. »
Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
12 Je discernai, et voici, Dieu ne l'avait pas envoyé, mais il prononçait cette prophétie contre moi. Tobija et Sanballat l'avaient engagé.
Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
13 Ils l'avaient engagé pour que j'aie peur, que j'agisse ainsi et que je commette un péché, et pour qu'ils aient de quoi faire un mauvais rapport, afin de m'accabler de reproches.
An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
14 « Souviens-toi, mon Dieu, de Tobija et de Sanballat selon leurs œuvres, et aussi de la prophétesse Noadia et du reste des prophètes qui auraient voulu me faire peur. »
Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
15 Et la muraille fut achevée le vingt-cinquième jour d'Eloul, en cinquante-deux jours.
Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
16 Lorsque tous nos ennemis l'apprirent, toutes les nations qui nous entouraient eurent peur et perdirent leur confiance, car elles comprirent que cette œuvre avait été faite par notre Dieu.
Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
17 En ce temps-là, les nobles de Juda envoyèrent de nombreuses lettres à Tobija, et les lettres de Tobija leur parvenaient.
A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
18 Car il y en avait beaucoup en Juda qui lui juraient fidélité, parce qu'il était gendre de Shecania, fils d'Arach, et que son fils Jehohanan avait pris pour femme la fille de Meshullam, fils de Bérékia.
Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
19 Ils parlèrent aussi de ses bonnes actions devant moi, et lui rapportèrent mes paroles. Tobija envoya des lettres pour me faire peur.
Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.

< Néhémie 6 >