< Néhémie 3 >

1 Alors Eliashib, le grand prêtre, se leva avec ses frères les prêtres, et ils construisirent la porte des brebis. Ils la sanctifièrent et en posèrent les portes. Ils la sanctifièrent jusqu'à la tour de Hammea, jusqu'à la tour de Hananel.
Eliyashib babban firist da’yan’uwansa firistoci suka tashi suka sāke gina Ƙofar Tumaki. Suka tsarkake ta, suka sa ƙofofinta a wurarensu, suka yi ginin har Hasumiyar Ɗari, wadda suka tsarkake, da kuma Hasumiyar Hananel.
2 A côté de lui, les hommes de Jéricho bâtirent. A côté d'eux, Zaccur, fils d'Imri, bâtit.
Mutanen Yeriko kuwa suka kama ginin daga mahaɗin, Zakkur ɗan Imri kuma ya fara ginin biye da su.
3 Les fils de Hasséna construisirent la porte des poissons. Ils posèrent ses poutres, ses portes, ses verrous et ses barres.
’Ya’yan Hassenaya ne suka gina Ƙofar Kifi. Suka kafa ginshiƙan, suka kuma sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu.
4 A côté d'eux, Meremoth, fils d'Urie, fils de Hakkoz, fit des réparations. A côté d'eux, Meshullam, fils de Bérékia, fils de Meshezabel, fit des réparations. A côté d'eux, Zadok, fils de Baana, répara.
Kusa da su kuma, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz ne ya yi gyare-gyaren. Biye da shi kuma sai Meshullam ɗan Berekiya, ɗan Meshezabel ya yi gyare-gyare. Kusa da shi Zadok ɗan Ba’ana shi ma ya yi gyare-gyare.
5 A côté d'eux, les Tekoïtes réparaient; mais leurs nobles ne mettaient pas leur cou à l'ouvrage du Seigneur.
Mutanen Tekowa ne suka yi gyare-gyare biye da shi, amma manyan garinsu suka ƙi su sa hannu cikin aikin da shugabanninsu suka bayar.
6 Joiada, fils de Paseah, et Meshullam, fils de Besodeiah, réparèrent la vieille porte. Ils en posèrent les poutres et en placèrent les portes, les verrous et les barres.
Yohiyada ɗan Faseya, da Meshullam ɗan Besodehiya ne suka gyara Ƙofar Yeshana. Suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.
7 A côté d'eux, Melatia, le Gibéonite, et Jadon, le Méronothite, hommes de Gibéon et de Mitspa, réparèrent la résidence du gouverneur au-delà du fleuve.
Biye da su, mutanen Gibeyon da Mizfa Melatiya na Gibeyon da Yadon Meronot waɗanda suke ƙarƙashin ikon gwamnan Kewayen Kogin Yuferites ne suka yi gyare-gyaren.
8 A côté de lui, Uzziel, fils de Harhaïa, orfèvres, effectuèrent des réparations. A côté de lui, Hanania, l'un des parfumeurs, fit des réparations, et ils fortifièrent Jérusalem jusqu'à la grande muraille.
Uzziyel ɗan Harhahiya, ɗaya daga cikin masu ƙeran zinariya ne ya yi gyare-gyaren sashe na biye; sai Hananiya, ɗaya daga cikin masu yin turare, ya yi gyare-gyaren biye da wannan. Suka gyara Urushalima har zuwa Katanga Mai Faɗi.
9 A côté d'eux, Rephaïa, fils de Hur, chef de la moitié du district de Jérusalem, fit des réparations.
Refahiya ɗan Hur, mai mulkin rabin yankin Urushalima, ya yi gyare-gyaren sashe na biye.
10 A côté d'eux, Jedaiah, fils de Harumaph, fit des réparations en face de sa maison. A côté de lui, Hattush, fils d'Hashabneia, répara.
Kusa da Refahiya, Yedahiya ɗan Harumaf ya yi gyare-gyaren daga gaban gidansa, sai Hattush ɗan Hashabnehiya ya yi gyare-gyaren biye da shi.
11 Malkija, fils de Harim, et Hasshub, fils de Pahathmoab, réparèrent une autre partie et la tour des fours.
Malkiya ɗan Harim, da Hasshub ɗan Fahat-Mowab ya yi gyare-gyaren wani sashe da kuma Hasumiyar Wurin Gashi.
12 A côté de lui, Shallum, fils de Hallohesh, chef de la moitié du district de Jérusalem, et ses filles réparèrent.
Shallum ɗan Hallohesh, mai mulkin ɗayan rabin yankin Urushalima ya yi gyare-gyaren sashe na biye tare da taimakon’ya’yansa mata.
13 Hanun et les habitants de Zanoa réparèrent la porte de la vallée. Ils la construisirent et mirent en place ses portes, ses verrous et ses barres, ainsi que mille coudées de mur jusqu'à la porte du fumier.
Hanun da mazaunan Zanowa ne suka gyara Ƙofar Kwari. Suka sāke gina ta suka sa ƙofofinta, da sakatunta, da sandunan ƙarfenta a wurarensu. Suka kuma gyara yadi ɗari biyar na katangar har zuwa Ƙofar Juji.
14 Malkija, fils de Rechab, chef du district de Beth Haccherem, répara la porte des fumiers. Il l'a construite et a mis en place ses portes, ses verrous et ses barres.
Malkiya ɗan Rekab mai mulkin yankin Bet-Hakkerem ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Juji. Ya sāke gina ta ya kuma sa sakatunta, da sanduna ƙarfenta a wurarensu.
15 Shallun, fils de Colhozeh, chef du district de Mitspa, répara la porte de la source. Il la construisit, la couvrit et en posa les portes, les verrous et les barres. Il répara aussi le mur de l'étang de Shéla, près du jardin du roi, jusqu'à l'escalier qui descend de la cité de David.
Shallum ɗan Kol-Hoze mai mulkin Mizfa ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Maɓuɓɓuga. Ya sāke gina ta, ya yi mata jinƙa yana sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu. Ya kuma gyara katangar tafkin Silowam, ta Lambun Sarki, har zuwa matakalan da suka gangara daga Birnin Dawuda.
16 Après lui, Néhémie, fils d'Azbuk, chef de la moitié du district de Beth Tsur, répara le lieu situé en face des tombeaux de David, l'étang qui avait été construit et la maison des héros.
Gaba da shi, Nehemiya ɗan Azbuk, mai mulkin rabin yankin Bet-Zur ne ya yi gyare-gyaren har zuwa kusa da kaburburan Dawuda, har zuwa haƙaƙƙen tafki da kuma Gidan Jarumawa.
17 Après lui, les Lévites - Rehum, fils de Bani - firent des réparations. A côté de lui, Haschabia, chef de la moitié du district de Keïla, fit des réparations pour son district.
Biye da shi, Lawiyawa a ƙarƙashin Rehum ɗan Bani ne suka yi gyare-gyaren. Kusa da su, Hashabiya mai mulkin rabin yankin Keyila ne ya yi gyare-gyaren don yankinsa.
18 Après lui, leurs frères, Bavvai, fils de Henadad, chef de la moitié du district de Keila, répara.
Biye da shi,’yan’uwansu Lawiyawa ne a ƙarƙashin Binnuyi ɗan Henadad, mai mulkin ɗayan rabin yankin Keyila suka yi gyare-gyaren.
19 A côté de lui, Ezer, fils de Jeshua, chef de Mitspa, répara une autre portion, en face, depuis la montée jusqu'à l'arsenal, au tournant de la muraille.
Biye da su, Ezer ɗan Yeshuwa, mai mulkin Mizfa, ya yi gyara wani sashe, daga inda yake fuskantar hawan gidan makamai har zuwa kusurwa.
20 Après lui, Baruch, fils de Zabbai, répara avec ardeur une autre portion, depuis le tournant du mur jusqu'à la porte de la maison du grand prêtre Eliashib.
Biye da shi, Baruk ɗan Zakkai da ƙwazo ya gyara wani sashe, daga kusurwa zuwa mashigin gidan Eliyashib babban firist.
21 Après lui, Merémoth, fils d'Urie, fils de Hakkoz, répara une autre portion, depuis la porte de la maison d'Éliaschib jusqu'à l'extrémité de la maison d'Éliaschib.
Biye da shi, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz, ya yi gyaran wani sashe, daga mashigin gidan Eliyashib zuwa ƙarshensa.
22 Après lui, les prêtres, les hommes des environs firent des réparations.
Firistoci daga kewayen yankin ne suka yi gyare-gyaren biye da shi.
23 Après eux, Benjamin et Hasshub firent des réparations en face de leur maison. Après eux, Azaria, fils de Maaséja, fils d'Anania, répara à côté de sa maison.
Can gaba da su, Benyamin da Hasshub ne suka yi gyare-gyaren a gaban gidansu, biye da su kuwa, Azariya ɗan Ma’asehiya, ɗan Ananiya ne ya yi gyare-gyaren kusa da gidansa.
24 Après lui, Binnui, fils de Hénadad, répara une autre portion, depuis la maison d'Azaria jusqu'au tournant du mur et jusqu'à l'angle.
Biye da shi, Binnuyi ɗan Henadad ya yi gyaran wani sashe, daga gidan Azariya zuwa kusurwa,
25 Palal, fils d'Uzai, répara l'angle de la muraille et la tour qui s'élève de la maison haute du roi, près de la cour des gardes. Après lui, Pedaja, fils de Parosh, fit des réparations.
sai Falal ɗan Uzai ya yi aiki ɗaura da kusurwa da kuma doguwar hasumiya daga fadar da take bisa kusa da shirayin masu tsaro. Biye da shi, Fedahiya ɗan Farosh
26 (Les serviteurs du temple habitaient à Ophel, à l'endroit situé en face de la porte des eaux, vers l'est, et de la tour qui se dresse).
da masu hidimar haikali da suke zama a tudun Ofel ne suka yi gyare-gyaren har zuwa wani wuri ɗaura da Ƙofar Ruwa wajen gabas da kuma doguwar hasumiya.
27 Après lui, les Tekoïtes réparèrent une autre partie, en face de la grande tour qui se dresse, et jusqu'au mur d'Ophel.
Biye da su, mutanen Tekowa suka yi gyaran wani sashe, daga babbar doguwar hasumiya zuwa katangar Ofel.
28 Au-dessus de la porte des chevaux, les sacrificateurs réparaient, chacun en face de sa maison.
Daga Ƙofar Doki, firistoci ne suka yi gyare-gyaren, kowanne a gaban gidansa.
29 Après eux, Zadok, fils d'Immer, réparait en face de sa maison. Après lui, Shemaya, fils de Shecania, gardien de la porte orientale, fit des réparations.
Biye da su, Zadok ɗan Immer ya yi gyare-gyaren ɗaura da gidansa. Biye da shi, Shemahiya ɗan Shekaniya, mai tsaron Ƙofar Gabas ya yi gyare-gyare.
30 Après lui, Hanania, fils de Shemiah, et Hanun, sixième fils de Zalaph, réparèrent une autre portion. Après lui, Meshullam, fils de Bérékia, répara la partie située en face de sa chambre.
Biye da shi, Hananiya ɗan Shelemiya, da Hanun, ɗa na shida na Zalaf, suka gyara wani sashe. Biye da su, Meshullam ɗan Berekiya ya yi gyare-gyaren ɗaura da wurin zamansa.
31 Après lui, Malkija, l'un des orfèvres de la maison des serviteurs du temple et des marchands, répara en face de la porte d'Hammiphkad et jusqu'à la montée de l'angle.
Biye da shi, Malkiya, ɗaya daga cikin masu ƙera zinariya ya yi gyare-gyaren har zuwa gidan masu hidimar haikali da kuma’yan kasuwa, ɗaura da Ƙofar Bincike, har zuwa ɗakin da yake bisa kusurwar.
32 Entre la montée de l'angle et la porte des brebis, les orfèvres et les marchands firent des réparations.
Maƙeran zinariya da’yan kasuwa suka gyara wani sashi tsakanin ɗakin da yake bisa kusurwa da Ƙofar Tumaki.

< Néhémie 3 >