< Néhémie 13 >

1 Ce jour-là, on lut dans le livre de Moïse, à l'oreille du peuple, et l'on trouva écrit qu'un Ammonite et un Moabite ne devaient pas entrer à jamais dans l'assemblée de Dieu,
A wannan rana aka karanta Littafin Musa da ƙarfi a kunnuwan mutane aka kuma sami an rubuta cewa kada a karɓi mutumin Ammon ko mutumin Mowab cikin taron Allah,
2 parce qu'ils n'allaient pas au-devant des enfants d'Israël avec du pain et de l'eau, mais qu'ils engageaient contre eux Balaam pour les maudire; cependant, notre Dieu changea la malédiction en bénédiction.
domin ba su taryi Isra’ila da abinci da ruwa ba amma suka yi hayar Bala’am don yă kira la’ana a kansu. (Amma Allahnmu, ya mai da la’anar ta zama albarka.)
3 Lorsqu'ils eurent entendu la loi, ils séparèrent d'Israël toute la multitude mélangée.
Sa’ad da mutane suka ji wannan doka, sai suka ware daga Isra’ila duk waɗanda suke na baƙon zuriya.
4 Avant cela, le prêtre Éliaschib, qui était préposé aux chambres de la maison de notre Dieu, étant allié à Tobija,
Kafin wannan, an sa Eliyashib firist yă lura da ɗakuna ajiyar gidan Allahnmu. Yana da dangantaka na kurkusa da Tobiya,
5 avait préparé pour lui une grande salle, où l'on déposait les offrandes, l'encens, les vases, les dîmes du blé, du vin nouveau et de l'huile, qui étaient donnés par ordre aux Lévites, aux chantres et aux portiers, et les offrandes d'ondulations pour les prêtres.
ya kuma tanada masa babban ɗakin da dā ake ajiyar hadayun hatsi da turare da kayayyaki haikali, da kuma zakan hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai da aka umarta don Lawiyawa, mawaƙa da kuma matsaran ƙofofi, da kuma sadakoki domin firistoci.
6 Mais en tout cela, je n'étais pas à Jérusalem; car la trente-deuxième année d'Artaxerxès, roi de Babylone, je me rendis auprès du roi; quelques jours après, je demandai congé au roi,
Amma yayinda dukan wannan yake faruwa, ba ni a Urushalima, gama a shekara ta talatin da biyu na Artazerzes sarkin Babilon na dawo wurin sarki. A wani lokaci daga baya na nemi izininsa
7 et j'arrivai à Jérusalem, où je compris le mal qu'Eliashib avait fait à Tobija, en lui préparant une chambre dans les parvis de la maison de Dieu.
sai na koma zuwa Urushalima. A nan na ji game da mugun abin da Eliyashib ya aikata da ya tanada wa Tobiya ɗaki a filayen gidan Allah.
8 Cela m'a beaucoup peiné. C'est pourquoi j'ai jeté hors de la chambre tous les effets personnels de Tobija.
Na ɓace rai ƙwarai na kuma zubar da dukan kayan gidan Tobiya daga ɗakin.
9 Puis j'ai donné des ordres, et on a nettoyé les chambres. J'y apportai les vases de la maison de Dieu, avec les offrandes de repas et l'encens de nouveau.
Na umarta a tsarkake ɗakunan, sa’an nan na mayar da kayan gidan Allah a cikin ɗakunan, tare da hadayun hatsi da kuma turare.
10 Je m'aperçus que les parts des Lévites ne leur avaient pas été données, de sorte que les Lévites et les chantres, qui faisaient le travail, s'étaient enfuis chacun dans son champ.
Na kuma ji cewa sassan da ake ba wa Lawiyawa ba a ba su ba, cewa kuma dukan Lawiyawa da mawaƙan da suke da hakkin hidima sun koma gonakinsu.
11 Alors je contestai avec les chefs, et je dis: « Pourquoi la maison de Dieu est-elle abandonnée? » Je les rassemblai et les remis à leur place.
Sai na tsawata wa shugabanni na kuma tambaye su na ce, “Me ya sa aka ƙyale gidan Allah?” Sa’an nan na kira su gaba ɗaya na sa su a wuraren aikinsu.
12 Alors tout Juda apporta aux trésors la dîme du blé, du vin nouveau et de l'huile.
Dukan Yahuda suka kawo zakan hatsi, sabon ruwan inabi da mai cikin ɗakunan ajiya.
13 J'établis comme trésoriers des trésors le sacrificateur Schélémia, le scribe Tsadok, et Pedaja, l'un des Lévites; Hanan, fils de Zaccur, fils de Matthania, était à côté d'eux, car ils étaient considérés comme fidèles, et leur tâche était de distribuer à leurs frères.
Na sa Shelemiya firist, Zadok marubuci, da wani Balawe mai suna Fedahiya su lura da ɗakunan ajiya na kuma sa Hanan ɗan Zakkur, ɗan Mattaniya ya zama mataimakinsu, domin an ɗauka waɗannan mutane amintattu ne. Aka ba su hakkin raban kayayyaki wa’yan’uwansu.
14 Souviens-toi de moi, mon Dieu, à propos de ceci, et n'efface pas mes bonnes actions que j'ai faites pour la maison de mon Dieu et pour ses observances.
Ka tuna da ni saboda wannan, ya Allahna, kuma kada ka shafe abin da na yi da aminci domin gidan Allahna da kuma hidimarsa.
15 En ce temps-là, j'ai vu en Juda des hommes qui foulaient des pressoirs le jour du sabbat, qui apportaient des gerbes et chargeaient des ânes de vin, de raisins, de figues et de toutes sortes de fardeaux qu'ils apportaient à Jérusalem le jour du sabbat; et j'ai rendu témoignage contre eux le jour où ils vendaient des aliments.
A waɗannan kwanaki, na ga mutane a Yahuda suna matse ruwan inabi a ranar Asabbaci suna kuma kawo hatsi suna labta su a kan jakuna, tare da ruwan inabi,’ya’yan inabi, ɓaure da kaya iri-iri. Suna kuma kawowa dukan wannan cikin Urushalima a ranar Asabbaci. Saboda haka na gargaɗe su a kan sayar da abinci a wannan rana.
16 Il y avait là aussi des hommes de Tyr, qui apportaient du poisson et toutes sortes de marchandises, et vendaient le jour du sabbat aux enfants de Juda et à Jérusalem.
Mutane daga Taya waɗanda suke zama a Urushalima suna shigar da kifi da kaya iri-iri na’yan kasuwa suna kuma sayar da su a Urushalima a ranar Asabbaci wa mutanen Yahuda.
17 Alors je contestai avec les nobles de Juda, et je leur dis: « Quelle est cette mauvaise action que vous faites, et qui consiste à profaner le jour du sabbat?
Sai na tsawata wa manyan Yahuda na ce musu, “Wanda irin mugun abu ke nan kuke yi, kuna ƙazantar da ranar Asabbaci?
18 Vos pères n'ont-ils pas fait cela, et notre Dieu n'a-t-il pas fait venir tout ce mal sur nous et sur cette ville? Mais vous attirez encore plus de colère sur Israël en profanant le sabbat. »
Kakanninku ba su yi irin waɗannan abubuwa ba, har Allahnmu ya kawo dukan masifun nan a kanmu da kuma a kan wannan birni? Yanzu kuna tsokanar fushi mai yawa a kan Isra’ila ta wurin ƙazantar da Asabbaci.”
19 Lorsque les portes de Jérusalem commencèrent à s'obscurcir avant le sabbat, j'ordonnai de fermer les portes et de ne les ouvrir qu'après le sabbat. Je confiai la surveillance des portes à quelques-uns de mes serviteurs, afin qu'aucun fardeau ne soit introduit le jour du sabbat.
Sa’ad da inuwar yamma ya fāɗo a ƙofofin Urushalima kafin Asabbaci, na umarta a rufe ƙofofi kuma kada a buɗe sai Asabbaci ya wuce. Na kafa waɗansu mutanena a ƙofofin don kada a shigo da wani kaya a ranar Asabbaci.
20 Les marchands et les vendeurs de toutes sortes de marchandises campaient donc une ou deux fois devant Jérusalem.
Sau ɗaya ko biyu,’yan kasuwa da masu sayar da kowane irin kaya suka kwana waje da Urushalima.
21 Je leur rendis alors témoignage et leur dis: « Pourquoi restez-vous autour de la muraille? Si vous le faites encore, je mettrai la main sur vous. » À partir de ce moment-là, ils ne vinrent plus le jour du sabbat.
Amma na ja kunnensu na ce, “Me ya sa kuke kwana kusa da katanga? In kuka ƙara yin haka, zan kama ku.” Daga wannan lokaci har zuwa gaba ba su ƙara zuwa a ranar Asabbaci ba.
22 J'ai ordonné aux Lévites de se purifier et de venir garder les portes, afin de sanctifier le jour du sabbat. Souviens-toi de moi pour cela aussi, mon Dieu, et épargne-moi selon la grandeur de ta bonté.
Sai na umarci Lawiyawa su tsarkake kansu su kuma tafi su yi tsaron ƙofofi don a kiyaye ranar Asabbaci da tsarki. Ka tuna da ni saboda wannan shi ma, ya Allahna, ka nuna mini jinƙai bisa ga madawwamiyar ƙaunarka.
23 En ce temps-là, je vis aussi des Juifs qui avaient épousé des femmes d'Asdod, d'Ammon et de Moab;
Ban da haka, a waɗannan kwanakin na ga mutanen Yahuda waɗanda suka auri mata daga Ashdod, Ammon da Mowab.
24 et leurs enfants parlaient à demi dans la langue d'Asdod, et ne pouvaient parler dans la langue des Juifs, mais selon la langue de chaque peuple.
Rabin’ya’yansu suna yaren Ashdod ko kuwa wani yare na waɗansu mutane, ba su kuwa san yadda za su yi Yahudanci ba.
25 Je les disputai, je les maudis, je frappai quelques-uns d'entre eux, j'arrachai leurs cheveux, et je leur fis jurer par Dieu: Vous ne donnerez pas vos filles à leurs fils, et vous ne prendrez pas leurs filles pour vos fils ou pour vous-mêmes.
Na tsawata musu na kuma kira la’ana a kansu. Na bugi waɗansu mutane na kuma ja gashin kansu. Na sa suka yi rantsuwa da sunan Allah na ce, “Kada ku ba da’ya’yanku mata aure ga’ya’yansu maza, ba kuwa za ku auri’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza ko wa kanku ba.
26 Salomon, roi d'Israël, n'a-t-il pas péché par ces choses? Pourtant, parmi les nombreuses nations, il n'y avait pas de roi comme lui, et il était aimé de son Dieu, et Dieu l'a établi roi sur tout Israël. Mais les femmes étrangères l'ont fait pécher, lui aussi.
Ba don aure-aure irin waɗannan ne Solomon sarkin Isra’ila ya yi zunubi ba? A cikin yawancin al’ummai babu sarki kamar sa. Allahnsa ya ƙaunace shi, Allah kuma ya mai da shi sarki a kan dukan Isra’ila, amma duk da haka baren mata suka rinjaye shi ga zunubi.
27 Allons-nous donc vous écouter pour faire tout ce grand mal, pour transgresser notre Dieu en épousant des femmes étrangères? ".
Yanzu za mu ji cewa ku ma kuna yin duk wannan mugunta kuna zama marasa aminci ga Allahnmu ta wurin auren baren mata?”
28 L'un des fils de Jojada, fils d'Eliashib, le grand prêtre, était gendre de Sanballat, le Horonite; c'est pourquoi je l'ai chassé de moi.
Ɗaya daga cikin’ya’yan Yohiyada maza, ɗan Eliyashib babban firist, surukin Sanballat mutumin Horon ne. Na kuwa kore shi daga wurina.
29 Souviens-toi d'eux, mon Dieu, car ils ont souillé le sacerdoce et l'alliance du sacerdoce et des Lévites.
Ka tuna da su, ya Allahna, domin sun ƙazantar da aikin firist da kuma alkawarin aikin firist da na Lawiyawa.
30 C'est ainsi que je les ai purifiés de tout étranger et que j'ai établi des fonctions pour les prêtres et les lévites, chacun dans son travail;
Saboda haka na tsarkake firistoci da Lawiyawa daga kowane baƙon abu, na kuma ba su aikinsu, kowa ga aikinsa.
31 ainsi que pour l'offrande de bois, aux temps fixés, et pour les prémices. Souviens-toi de moi, mon Dieu, pour le bien.
Na kuma yi tanadi don sadakokin itace a ƙayyadaddun lokuta, da kuma don nunan fari. Ka tuna da ni da alheri, ya Allahna.

< Néhémie 13 >