< Malachie 3 >

1 « Voici, j'envoie mon messager, et il préparera le chemin devant moi! Le Seigneur, que vous cherchez, viendra soudain dans son temple. Voici que vient le messager de l'alliance que tu désires, dit Yahvé des armées.
“Duba, zan aika manzona, wanda zai shirya hanya a gabana. Sa’an nan a farat ɗaya Ubangiji wanda kuke nema zai zo haikalinsa. Manzon alkawari, wanda kuke sa zuciya kuwa zai zo,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
2 « Mais qui pourra supporter le jour de son avènement? Et qui résistera quand il paraîtra? Car il est comme le feu d'un raffineur, et comme le savon d'un blanchisseur.
Amma wa zai jure wa ranar zuwansa? Wa zai iya tsaya sa’ad da ya bayyana? Gama zai zama kamar wuta mai tace ƙarfe, ko sabulu mai wanki.
3 Il s'assiéra comme un raffineur et un purificateur d'argent, et il purifiera les fils de Lévi, il les affinera comme l'or et l'argent, et ils offriront à Yahvé des offrandes en justice.
Zai zama kamar mai tace azurfa da mai tsarkaketa; zai tsabtacce Lawiyawa, yă kuma tace su kamar zinariya da azurfa. Sa’an nan Ubangiji zai sami mutanen da za su kawo hadayu a cikin adalci.
4 Alors l'offrande de Juda et de Jérusalem sera agréable à l'Éternel comme aux jours d'autrefois et comme dans les années passées.
Hadayun Yahuda da na Urushalima za su zama yardajje ga Ubangiji, za su zama kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a shekarun baya.
5 Je m'approcherai de vous pour vous juger. Je serai un témoin rapide contre les sorciers, contre les adultères, contre les parjures, contre ceux qui oppriment le mercenaire dans son salaire, la veuve et l'orphelin, et qui privent l'étranger de justice, et ne me craignent pas », dit Yahvé des armées.
“Ta haka zan zo kusa da ku don in yi hukunci. Zan hanzarta ba da shaida a kan masu yin sihiri, da mazinata da masu shaidar zur. Zan ba da shaida a kan waɗanda suke zaluntar ma’aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye da marayu, suna kuma hana baƙi samun adalci, ba sa ma tsorona,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
6 « Car moi, Yahvé, je ne change pas; c'est pourquoi vous, fils de Jacob, vous n'êtes pas consumés.
“Ni Ubangiji ba na canjawa. Shi ya sa ku zuriyar Yaƙub, ba a hallaka ku ƙaƙaf ba.
7 Depuis les jours de vos pères, vous vous êtes détournés de mes ordonnances et vous ne les avez pas gardées. Revenez à moi, et je reviendrai à vous », dit Yahvé des armées. Mais vous dites: « Comment reviendrons-nous?
Tun zamanin kakanninku, kun juye wa ƙa’idodina baya, ba ku kuma kiyaye su ba. Ku komo gare ni, ni kuma zan koma gare ku,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya za mu koma gare ka?’
8 Un homme volera-t-il Dieu? Mais vous me volez, moi! Mais vous dites: « Comment vous avons-nous volé? En payant la dîme et les offrandes.
“Mutum zai iya yi wa Allah fashi ne? Duk da haka kun yi mini fashi. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka yi maka fashi?’ “A wajen zakka da hadayu.
9 Vous êtes frappés de malédiction, car vous me dépouillez, vous, toute cette nation.
Kuna ƙarƙashin la’ana, dukan al’ummarku, domin kuna yin mini fashi.
10 Apportez toute la dîme dans le grenier, afin qu'il y ait de la nourriture dans ma maison, et mettez-moi maintenant à l'épreuve, dit l'Éternel des armées, si je ne vous ouvre pas les fenêtres du ciel, et si je ne vous déverse pas une bénédiction qu'il n'y aura pas assez de place pour elle.
Ku kawo dukan zakka cikin gidan ajiya, don a kasance da abinci a gidana. Ku gwada ni a wannan ku ga, ko ba zan buɗe taskokin sama in zubo muku albarka mai yawa, wadda har ba za ku rasa wurin sa ta ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
11 Je réprimanderai le dévoreur à cause de vous, et il ne détruira pas les fruits de votre sol; votre vigne ne jettera pas son fruit avant son temps dans le champ, dit Yahvé des armées.
Zan hana ƙwari su cinye hatsinku. Kuringar inabi a gonakinku kuma ba za su zubar da’ya’yansu kafin su nuna ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
12 « Toutes les nations te diront bienheureux, car tu seras un pays de délices », dit Yahvé des armées.
“Sa’an nan dukan al’ummai za su ce da ku masu albarka, gama ƙasarku za tă yi daɗin zama,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
13 Vos paroles ont été dures à mon égard, dit l'Éternel.
“Kun faɗi mugayen abubuwa a kaina,” in ji Ubangiji. “Duk da haka kuka ce, ‘Me muka faɗa a kanka?’
14 Vous avez dit: « C'est en vain que l'on sert Dieu », et « Quel avantage y a-t-il à suivre ses instructions et à marcher dans le deuil devant l'Éternel des armées?
“Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Allah. Wanda amfani muka samu ta wurin kiyaye umarnansa muna yawo kamar masu makoki a gaban Ubangiji Maɗaukaki?
15 Maintenant, nous appelons les orgueilleux heureux; oui, ceux qui font le mal sont édifiés; oui, ils tentent Dieu, et ils échappent.''
A ganinmu, masu girman kai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suka yi ba, amma sukan gwada Allah da mugayen ayyukansu, su kuwa zauna lafiya.’”
16 Alors ceux qui craignaient l'Éternel se parlèrent entre eux; et l'Éternel écouta et entendit, et un livre de souvenir fut écrit devant lui pour ceux qui craignaient l'Éternel et qui honoraient son nom.
Sa’an nan waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da juna, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya kuma ji. A gabansa aka rubuta a littafin tarihi waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuma girmama sunansa.
17 Ils seront à moi, dit l'Éternel des armées, ma propriété, au jour que je ferai. Je les épargnerai, comme un homme épargne son propre fils qui le sert.
“A ranar da na shirya ajiyayyen mallakata, za su zama nawa,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ji kansu kamar yadda mahaifi cikin tausayi yakan ji kan ɗansa wanda yake masa hidima.
18 Alors vous reviendrez et vous discernerez entre le juste et le méchant, entre celui qui sert Dieu et celui qui ne le sert pas.
Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.

< Malachie 3 >