< Lévitique 22 >
1 Yahvé parla à Moïse, et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 « Dis à Aaron et à ses fils de se séparer des choses saintes des enfants d'Israël, qu'ils me consacrent, et de ne pas profaner mon saint nom. Je suis Yahvé.
“Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
3 « Dis-leur: « Si quelqu'un de tous vos descendants, de génération en génération, s'approche des choses saintes que les enfants d'Israël consacrent à Yahvé, en ayant sur lui son impureté, cette personne sera retranchée de devant moi. Je suis Yahvé.
“Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
4 "'Quiconque, parmi les descendants d'Aaron, est lépreux ou a des pertes, ne mangera pas des choses saintes jusqu'à ce qu'il soit pur. Celui qui touchera une chose souillée par un mort, ou un homme qui a une émission séminale,
“‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
5 ou celui qui touchera un reptile par lequel il peut être souillé, ou un homme de qui il peut être souillé, quelle que soit sa souillure -
da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
6 celui qui aura touché l'une de ces choses sera souillé jusqu'au soir, et ne mangera pas des choses saintes, à moins qu'il ne se lave le corps dans l'eau.
duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
7 Au coucher du soleil, il sera pur; ensuite, il mangera des choses saintes, car c'est son pain.
Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
8 Il ne mangera pas de ce qui meurt de lui-même ou qui est déchiré par les animaux, car il s'en souillerait. Je suis Yahvé.
Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
9 "'Ils suivront donc mon commandement, de peur de porter un péché à cause de lui et de mourir en lui, s'ils le profanent. C'est moi, Yahvé, qui les sanctifie.
“‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
10 "'Aucun étranger ne mangera de la chose sainte: un étranger qui habite avec les prêtres, ou un mercenaire, ne mangera pas de la chose sainte.
“‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
11 Mais si un prêtre achète un esclave, acquis par son argent, il en mangera; et ceux qui sont nés dans sa maison mangeront de son pain.
Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
12 Si la fille d'un prêtre est mariée à un étranger, elle ne mangera pas de l'offrande par élévation des choses saintes.
In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
13 Mais si la fille d'un prêtre est veuve ou divorcée, qu'elle n'a pas d'enfant et qu'elle est retournée dans la maison de son père comme dans sa jeunesse, elle pourra manger le pain de son père, mais aucun étranger n'en mangera.
Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
14 "'Si un homme mange involontairement une chose sainte, il y ajoutera le cinquième de sa valeur, et il donnera la chose sainte au prêtre.
“‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
15 Les prêtres ne profaneront pas les choses saintes des enfants d'Israël, qu'ils offrent à l'Éternel,
Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
16 et ne leur feront pas porter l'iniquité qui les rend coupables lorsqu'ils mangent leurs choses saintes, car je suis l'Éternel qui les sanctifie.'"
ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
17 Yahvé parla à Moïse, et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 Parle à Aaron, à ses fils et à tous les enfants d'Israël, et tu leur diras: « Si quelqu'un de la maison d'Israël ou des étrangers en Israël présente une offrande, qu'il s'agisse d'un de leurs vœux ou d'une de leurs offrandes volontaires, qu'ils offrent à Yahvé en holocauste:
“Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
19 Afin que tu sois agréé, tu offriras un mâle sans défaut, parmi les taureaux, les moutons ou les chèvres.
dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
20 Mais tu n'offriras pas ce qui a un défaut, car cela ne sera pas agréé pour toi.
Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
21 Celui qui offrira à Yahvé un sacrifice d'actions de grâces pour l'accomplissement d'un vœu, ou pour une offrande volontaire du gros ou du menu bétail, sera parfait pour être accepté. Il n'aura aucun défaut.
Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
22 Tu n'offriras pas à l'Éternel un aveugle, un blessé, un mutilé, une verrue, un suppurant ou un ulcère, et tu n'en feras pas un sacrifice par le feu sur l'autel de l'Éternel.
Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
23 Soit un taureau ou un agneau qui a une difformité ou un défaut de ses parties, que vous pourrez offrir en offrande volontaire; mais pour un vœu, il ne sera pas accepté.
Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
24 Vous n'offrirez pas à Yahvé ce qui a les testicules meurtris, écrasés, cassés ou coupés. Vous ne ferez pas cela dans votre pays.
Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
25 Vous n'offrirez rien de tout cela comme pain de votre Dieu, de la main d'un étranger, car il y a en eux de la corruption. Il y a en eux un défaut. Ils ne seront pas acceptés pour vous. »"
Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
26 Yahvé parla à Moïse et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
27 « Lorsqu'un taureau, un mouton ou une chèvre naîtra, il restera sept jours avec sa mère. A partir du huitième jour, il sera accepté pour l'offrande d'un sacrifice consumé par le feu à Yahvé.
“Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
28 Qu'il s'agisse d'une vache ou d'une brebis, vous ne l'égorgerez pas avec son petit en un seul jour.
Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
29 « Lorsque tu offriras un sacrifice d'action de grâces à Yahvé, tu le sacrifieras pour être agréé.
“Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
30 Il sera mangé le jour même; tu n'en laisseras rien jusqu'au matin. Je suis Yahvé.
Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
31 « C'est pourquoi vous garderez mes commandements et vous les mettrez en pratique. Je suis Yahvé.
“Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
32 Vous ne profanerez pas mon saint nom, mais je serai sanctifié au milieu des enfants d'Israël. Je suis Yahvé, qui vous rend saints,
Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
33 qui vous a fait sortir du pays d'Égypte, pour être votre Dieu. Je suis Yahvé. »
da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”