< Lévitique 20 >

1 Yahvé parla à Moïse et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Tu diras aux enfants d'Israël: « Si quelqu'un parmi les enfants d'Israël ou parmi les étrangers qui vivent en Israël donne un de ses descendants à Moloch, il sera puni de mort. Les habitants du pays lapideront cette personne.
“Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikin Isra’ila da ya miƙa wani daga cikin’ya’yansa wa Molek, dole sa kashe shi. Mutanen ƙasar za su jajjefe shi.
3 Moi aussi, je tournerai ma face contre cet homme, et je le retrancherai du milieu de son peuple, parce qu'il a donné de sa progéniture à Moloch, pour souiller mon sanctuaire et profaner mon saint nom.
Zan yi gāba da wannan mutum, zan kuma raba shi da mutanensa; gama ta wurin miƙa’ya’yansa ga Molek, ya ƙazantar da wuri mai tsarkina, ya kuma ƙazantar da sunana mai tsarki.
4 Si tous les habitants du pays cachent les yeux de cette personne lorsqu'elle donne de sa progéniture à Moloc, et ne la font pas mourir,
In mutanen ƙasar suka kau da idanunsu sa’ad da wannan mutum ya miƙa’ya’yansa ga Molek, suka kāsa kashe shi,
5 je tournerai ma face contre cet homme et contre sa famille, et je la retrancherai du milieu de son peuple, ainsi que tous ceux qui se prostituent après lui pour se prostituer à Moloc.
zan yi gāba da wannan mutum da iyalinsa, zan raba shi da kuma duk waɗanda suka bi shi cikin karuwanci ga Molek daga mutanensu.
6 "'Celui qui se tourne vers les médiums et les magiciens, pour se prostituer après eux, je tournerai ma face contre lui, et je le retrancherai du milieu de son peuple.
“‘Zan yi gāba da mutumin da ya juyo ga masu duba da bokaye, don yă yi karuwanci ta wurin bin su, zan kuma raba shi daga mutanensa.
7 « Sanctifiez-vous donc et soyez saints, car je suis Yahvé votre Dieu.
“‘Ku tsarkake kanku, ku kuma zama da tsarki, gama Ni ne Ubangiji Allahnku.
8 Vous observerez mes lois et vous les mettrez en pratique. C'est moi, Yahvé, qui vous sanctifie.
Ku kiyaye farillaina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
9 "'Car quiconque maudit son père ou sa mère sera puni de mort. Il a maudit son père ou sa mère. Son sang retombera sur lui.
“‘In wani ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi. Domin ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, alhakin jininsa zai zauna a kansa.
10 "'L'homme qui commet un adultère avec la femme d'un autre homme, même celui qui commet un adultère avec la femme de son prochain, l'adultère et la femme adultère seront punis de mort.
“‘In mutum ya yi zina da matar wani, da matar maƙwabcinsa, dole a kashe su biyu da suka yi zinan.
11 "'L'homme qui couche avec la femme de son père a découvert la nudité de son père. Ils seront tous deux mis à mort. Leur sang retombera sur eux.
“‘In mutum ya kwana da matar mahaifinsa, ya ƙasƙantar da mahaifinsa. Dole a kashe shi da macen, alhakin jininsu zai zauna a kansu.
12 "'Si un homme couche avec sa belle-fille, ils seront tous deux mis à mort. Ils ont commis une perversion. Leur sang retombera sur eux.
“‘In mutum ya kwana da matar ɗansa, dole a kashe su biyun. Abin da suka yi haram ne; alhakin jininsu zai zauna a kansu.
13 "'Si un homme couche avec un mâle, comme avec une femme, tous deux ont commis une abomination. Ils seront mis à mort. Leur sang retombera sur eux.
“‘In mutum ya kwana da mutum kamar yadda ake kwana da mace, su biyun sun yi abin ƙyama. Dole a kashe su, alhakin jininsu zai zauna a kansu.
14 "'Si un homme prend une femme et sa mère, c'est une infamie. Ils seront brûlés au feu, lui et elles, afin qu'il n'y ait pas de méchanceté parmi vous.
“‘In mutum ya auri’ya da mahaifiyarta, mugun abu ne. Da shi da su, dole a ƙone su da wuta, saboda kada mugun abu yă kasance a cikinku.
15 "'Si un homme couche avec un animal, il sera mis à mort, et vous tuerez l'animal.
“‘In mutum ya yi jima’i da dabba, dole a kashe shi, dole kuma ku kashe dabbar.
16 "'Si une femme s'approche d'un animal et couche avec lui, vous tuerez la femme et l'animal. Ils seront mis à mort. Leur sang retombera sur eux.
“‘In mace ta kusaci dabba don tă yi jima’i da ita, ku kashe macen da dabbar. Dole a kashe su; alhakin jininsu zai zauna a kansu.
17 "'Si un homme prend sa sœur, fille de son père ou fille de sa mère, et qu'il voit sa nudité, et qu'elle voit sa nudité, c'est une honte. Ils seront retranchés aux yeux des enfants de leur peuple. Il a découvert la nudité de sa sœur. Il portera son iniquité.
“‘In mutum ya auri’yar’uwarsa, ko’yar mahaifinsa, ko kuwa ta mahaifiyarsa, suka kuma yi jima’i, abin kunya ne. Dole a raba su a idanun mutanensu. Ya ƙasƙantar da’yar’uwarsa kuma za a nemi hakki daga gare shi.
18 "'Si un homme couche avec une femme qui a ses règles et découvre sa nudité, il a mis à nu sa source, et elle a découvert la source de son sang. Tous deux seront retranchés du milieu de leur peuple.
“‘In mutum ya kwana da mace a lokacin al’adarta, duka biyunsu za a kore su daga cikin jama’arsu, gama sun karya ƙa’idodi a kan rashi tsarki.
19 "'Tu ne découvriras pas la nudité de la sœur de ta mère, ni celle de la sœur de ton père, car il a mis à nu son proche parent. Ils porteront la peine de leur iniquité.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, ko ta mahaifinka, gama wannan zai ƙasƙantar da dangi na kurkusa, dukanku za ku ɗauki laifin.
20 Si un homme couche avec la femme de son oncle, il a découvert la nudité de son oncle. Ils porteront la peine de leur péché. Ils mourront sans enfant.
“‘In mutum ya kwana da bābarsa, ya ƙasƙantar da kawunsa ke nan. Hakkin zai kasance a kansu, za su mutu babu’ya’ya.
21 "'Si un homme prend la femme de son frère, c'est une impureté. Il a découvert la nudité de son frère. Ils seront sans enfants.
“‘In mutum ya auri matar ɗan’uwansa, aikin rashin tsabta ne, ya ƙasƙantar da ɗan’uwansa ke nan. Za su mutu babu’ya’ya.
22 "'Vous observerez donc toutes mes lois et toutes mes ordonnances, et vous les mettrez en pratique, afin que le pays où je vous fais habiter ne vous vomisse pas.
“‘Ku kiyaye dukan farillaina da dokokina duka, don kada ƙasar da nake kai ku ta amayar da ku.
23 Tu ne marcheras pas selon les coutumes de la nation que je rejette devant toi; car ils ont fait toutes ces choses, et c'est pourquoi je les ai en horreur.
Kada ku yi zama bisa ga al’adun al’umman da zan kora a gabanku. Domin sun aikata dukan waɗannan abubuwa, na yi ƙyamarsu.
24 Mais je vous ai dit: « Vous hériterez de leur pays, et je vous le donnerai en propriété, un pays où coulent le lait et le miel. » Je suis Yahvé, votre Dieu, qui vous a séparés des peuples.
Amma na faɗa muku, “Za ku mallaki ƙasarsu, zan ba ku ita gādo, ƙasa mai zub da madara da zuma.” Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya keɓe ku daga al’ummai.
25 "'Vous ferez donc la distinction entre l'animal pur et l'impur, et entre le volatile impur et le pur. Vous ne vous rendrez pas abominables par un animal, par un oiseau ou par tout ce dont regorge le sol, que j'ai séparé de vous comme impur pour vous.
“‘Saboda haka sai ku bambanta tsakanin dabbobi masu tsarki da marasa tsarki, da kuma tsakanin tsuntsaye masu tsarki da marasa tsarki. Kada ku ƙazantar da kanku ta wurin wata dabba, ko tsuntsu, ko wani abin da yake rarrafe a ƙasa, waɗanda na keɓe a matsayi marasa tsarki a gare ku.
26 Vous serez saints pour moi, car moi, Yahvé, je suis saint, et je vous ai séparés des peuples, pour que vous soyez à moi.
Ku zama tsarkakakke gare ni, gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, na kuma keɓe ku daga al’ummai don ku zama nawa.
27 "'Un homme ou une femme qui est un médium ou un magicien sera mis à mort. Ils seront lapidés. Leur sang retombera sur eux. »
“‘Namiji, ko ta macen da yake mai duba, ko maita a cikinku dole a kashe. Za ku jajjefe su da duwatsu; alhakin jininsu zai zauna a kansu.’”

< Lévitique 20 >