< Juges 8 >

1 Les hommes d'Éphraïm lui dirent: « Pourquoi nous as-tu traités de la sorte, en ne nous appelant pas quand tu es allé combattre Madian? » Ils le réprimandèrent vivement.
To, mutanen Efraim suka ce wa Gideyon, “Me ya sa ka yi mana haka? Me ya sa ba ka kira mu lokacin da ka tafi yaƙi da Midiyawa ba?” Suka zarge shi sosai.
2 Il leur répondit: « Qu'ai-je fait de plus que vous? La vendange d'Ephraïm ne vaut-elle pas mieux que celle d'Abiézer?
Amma ya ce musu, “Me na yi da za a iya kwatanta da abin da kuka yi? Ashe, kalar inabin da Efraim ta yi bai fi dukan girbin inabin da Abiyezer suka yi ba?
3 Dieu a livré entre vos mains les princes de Madian, Oreb et Zeeb! Qu'ai-je pu faire en comparaison de toi? » Leur colère s'apaisa à son égard après qu'il eut dit cela.
Allah ya ba da Oreb da Zeyib, shugabannin Midiyawa a hannuwanku. Me na yi da ya fi naku? Da ya faɗi haka sai hankalinsu ya kwanta.”
4 Gédéon arriva au Jourdain et le traversa, lui et les trois cents hommes qui étaient avec lui, faibles mais poursuivant.
Gideyon da mutanensa ɗari uku, sun gaji, duk da haka suka yi ta fafarar, suka zo Urdun suka haye shi.
5 Il dit aux hommes de Succoth: « Donnez, je vous prie, des pains aux gens qui me suivent, car ils sont épuisés, et je poursuis Zébah et Tsalmunna, les rois de Madian. »
Ya ce wa mutanen Sukkot, “Ku ba wa mutanena burodi; sun gaji, har yanzu ina fafarar Zeba da Zalmunna, sarakunan Midiyawa.”
6 Les princes de Succoth dirent: « Les mains de Zébah et de Tsalmunna sont-elles maintenant entre tes mains, pour que nous donnions du pain à ton armée? »
Amma shugabannin Sukkot suka ce, “Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Don me za mu ba wa mayaƙanka burodi?”
7 Gédéon dit: « C'est pourquoi, lorsque Yahvé aura livré entre mes mains Zébah et Tsalmunna, je déchirerai votre chair avec les épines du désert et avec les ronces. »
Sai Gideyon ya ce, “Haka ko? To, sa’ad da Ubangiji ya ba da Zeba da Zalmunna a hannuna, zan tsattsaga jikinku da ƙayayyuwan jeji.”
8 Il monta ensuite à Penuel, et leur parla de la même manière. Les hommes de Penuel lui répondirent comme les hommes de Succoth avaient répondu.
Daga nan ya wuce zuwa Fenuwel ya yi irin roƙon nan, amma suka amsa yadda mutanen Sukkot suka yi.
9 Il parla aussi aux hommes de Penuel, en disant: « Quand je reviendrai en paix, je démolirai cette tour. »
Saboda haka sai ya ce wa mutanen Fenuwel, “Sa’ad da na dawo da nasara zan rushe wannan hasumiya.”
10 Or Zébah et Tsalmunna étaient à Karkor, et leurs armées avec eux, environ quinze mille hommes, tous ceux qui restaient de toute l'armée des fils de l'Orient; car il tomba cent vingt mille hommes qui tirèrent l'épée.
To, Zeba da Zalmunna suna a Karkor da mayaƙa wajen dubu goma sha biyar, abin da ya rage ke nan na mayaƙan gabashi; mayaƙa masu takobi dubu ɗari da ashirin ne suka mutu.
11 Gédéon monta par le chemin de ceux qui habitaient dans des tentes à l'est de Nobah et de Jogbehah, et il frappa l'armée; car l'armée se sentait en sécurité.
Gideyon ya haura ta hanyar makiyaya, gabas da Noba, da kuma Yogbeha, ya fāɗa wa mayaƙan ta yadda ba su zata ba.
12 Zébah et Tsalmunna s'enfuirent et il les poursuivit. Il prit les deux rois de Madian, Zébah et Tsalmunna, et confondit toute l'armée.
Zeba da Zalmunna, sarakunan biyu na Midiyawa suka tsere, amma ya bi su ya kama, ya fatattaki dukan mayaƙansu.
13 Gédéon, fils de Joas, revint de la bataille par la montée de Hérès.
Sa’an nan Gideyon ɗan Yowash ya komo daga yaƙi ta Hanyar Heres.
14 Il prit un jeune homme parmi les hommes de Succoth, et le consulta; il lui décrivit les chefs de Succoth et ses anciens, soit soixante-dix-sept hommes.
Ya kama wani saurayin Sukkot ya tambaye shi, saurayin kuwa ya rubuta masa dukan sunayen shugabanni saba’in da bakwai na Sukkot, da dattawan garin.
15 Il s'approcha des hommes de Succoth et dit: « Voyez Zébah et Tsalmunna, au sujet desquels vous m'avez raillé en disant: « Les mains de Zébah et de Tsalmunna sont-elles maintenant entre vos mains, pour que nous donnions du pain à vos hommes qui sont fatigués? ».
Sa’an nan Gideyon ya zo ya ce wa mutanen Sukkot, “To, ga Zeba da Zalmunna, waɗanda kuka yi mini ba’a kuna cewa, ‘Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Me zai sa mu ba mutanenka da suka gaji burodi?’”
16 Il prit les anciens de la ville, des épines du désert et des ronces, et avec eux il enseigna aux hommes de Succoth.
Ya kwashe dattawan garin ya koya wa mutanen Sukkot hankali ta wurin hukunta su da ƙayayyuwan hamada.
17 Il démolit la tour de Penuel, et il tua les hommes de la ville.
Ya rushe hasumiyar Fenuwel ya kuma karkashe mutanen garin.
18 Puis il dit à Zébah et à Tsalmunna: « Quelle sorte d'hommes étaient ceux que vous avez tués au Thabor? » Ils répondirent: « Ils étaient comme vous. Ils ressemblaient tous aux enfants d'un roi. »
Sa’an nan ya ce wa Zeba da Zalmunna, “Waɗanne irin mutane ne kuka karkashe a Tabor.” Suka ce, “Mutane kamar ka ne kowane kamar ɗan sarki.”
19 Il répondit: « Ce sont mes frères, les fils de ma mère. L'Éternel est vivant, si tu les avais sauvés vivants, je ne te tuerais pas. »
Gideyon ya ce, “Waɗannan’yan’uwana ne,’ya’yan mahaifiyata. Muddin Ubangiji yana a raye, da a ce kun bar su da rai, da ba zan kashe ku ba.”
20 Il dit à Jether, son aîné: « Lève-toi et tue-les! » Mais le jeune homme ne tira pas son épée, car il avait peur, car il était encore jeune.
Da ya juya wajen Yeter, ɗan farinsa, sai ya ce, “Ka kashe su!” Amma Yeter bai zāre takobinsa ba, domin shi yaro ne kawai kuma yana tsoro.
21 Alors Zébah et Tsalmunna dirent: « Vous vous levez et vous tombez sur nous; car telle est la force de l'homme, telle est sa force. » Gédéon se leva, tua Zébah et Tsalmunna, et prit les croissants qui étaient au cou de leurs chameaux.
Zeba da Zalmunna suka ce masa, “Zo, ka yi da kanka. ‘Yadda mutum yake haka ƙarfinsa.’” Ta haka Gideyon ya matso gaba ya kashe su, ya ɗauki kayan ado daga wuyar raƙumansu.
22 Alors les hommes d'Israël dirent à Gédéon: « Domine sur nous, toi, ton fils et le fils de ton fils aussi, car tu nous as sauvés de la main de Madian. »
Isra’ilawa suka ce wa Gideyon, “Ka yi mulkinmu, kai, ɗanka da jikanka, domin ka cece mu daga hannun Midiyawa.”
23 Gédéon leur dit: « Je ne dominerai pas sur vous, et mon fils ne dominera pas sur vous. C'est Yahvé qui dominera sur vous. »
Amma Gideyon ya ce musu, “Ni, ko ɗana, ba za mu yi mulkinku ba. Ubangiji ne zai yi mulkinku.”
24 Gédéon leur dit: « J'ai une demande à faire: que chacun de vous me donne les boucles d'oreille de son butin. » (Car ils avaient des boucles d'oreilles en or, parce qu'ils étaient Ismaélites).
Kuma ya ce, “Ina da roƙo guda ɗaya, cewa kowannenku ya ba ni’yan kunne daga rabon ganima.” (Al’adar mutanen Ishmayel ce su sa’yan kunnen zinariya.)
25 Ils répondirent: « Nous les donnerons volontiers. » Ils étendirent un vêtement, et chacun y jeta les boucles d'oreilles de son butin.
Suka ce, “Za mu yi farin cikin ba ka su.” Saboda haka suka shimfiɗa mayafi, kowanne ya sa ɗan kunne ɗaya daga ganimar.
26 Le poids des boucles d'oreilles en or qu'il demanda était de mille sept cents sicles d'or, sans compter les croissants, les pendentifs, les vêtements de pourpre qui étaient sur les rois de Madian, et sans compter les chaînes qui étaient au cou de leurs chameaux.
Nauyin’yan kunnen zinariyar ya kai shekel ɗari goma sha bakwai, ban da kayan ado, abin wuya da tufafin shunayya waɗanda sarakuna Midiyawa suke sawa ko sarƙoƙin da suke wuyar raƙumansu.
27 Gédéon en fit un éphod, et le mit à Ophra, sa ville. Tout Israël s'y prostitua, et ce fut un piège pour Gédéon et pour sa maison.
Gideyon ya efod da zinariyar, wanda ya ajiye a Ofra, garinsa. Dukan Isra’ila suka shiga yin karuwanci ta wurin yin sujada a can, ya kuwa zama wa Gideyon da dukan iyalinsa tarko.
28 Ainsi Madian fut soumis aux enfants d'Israël, et ils ne levèrent plus la tête. Le pays fut en repos pendant quarante ans aux jours de Gédéon.
Da haka Isra’ilawa suka mallaki Midiyawa ba su kuma sāke tā da kai ba. A zamanin Gideyon ƙasar ta sami zaman lafiya har shekara arba’in.
29 Jerubbaal, fils de Joas, s'en alla et s'établit dans sa maison.
Yerub-Ba’al ɗan Yowash ya koma gida don yă zauna.
30 Gédéon eut soixante-dix fils conçus de son corps, car il avait beaucoup de femmes.
Yana da’ya’ya saba’in maza da ya haifa, gama yana da mata da yawa.
31 Sa concubine qui était à Sichem lui enfanta aussi un fils, et il l'appela Abimélec.
Yana kuma da ƙwarƙwara wadda take Shekem, ita ma ta haifa masa ɗa wanda ya ba shi suna Abimelek.
32 Gédéon, fils de Joas, mourut dans une bonne vieillesse, et il fut enterré dans le tombeau de Joas, son père, à Ophra, chez les Abiézrites.
Gideyon ɗan Yowash ya rasu da kyakkyawan tsufa aka kuma binne shi a kabarin Yowash mahaifinsa a Ofra na mutanen Abiyezer.
33 Dès que Gédéon fut mort, les enfants d'Israël se retournèrent, se prostituèrent aux Baals et firent de Baal Berith leur dieu.
Ba a daɗe da rasuwar Gideyon ba, sai Isra’ila ta sāke shiga karuwanci suna bauta wa Ba’al. Suka kafa Ba’al-Berit yă zama musu allahnsu ba kuma
34 Les enfants d'Israël ne se souvinrent pas de Yahvé, leur Dieu, qui les avait délivrés de la main de tous leurs ennemis de toute part;
tuna da Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga hannuwan abokan gābansu a kowane gefe ba.
35 et ils ne firent pas preuve de bonté envers la maison de Jerubbaal, c'est-à-dire Gédéon, selon toute la bonté qu'il avait montrée à Israël.
Suka kāsa nuna alheri ga gidan Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) saboda abubuwa masu alherin da ya yi musu.

< Juges 8 >