< Juges 18 >

1 En ce temps-là, il n'y avait pas de roi en Israël. En ces jours-là, la tribu des Danites chercha un héritage pour y habiter; car jusqu'à ce jour, leur héritage ne leur était pas échu parmi les tribus d'Israël.
To, a kwanakin nan Isra’ila ba ta da sarki. A kwanakin kuwa zuriyar Dan tana neman wurinsu na zama, gama ba su riga sun sami gādo tare da kabilan Isra’ila ba.
2 Les fils de Dan envoyèrent de Zorah et d'Eshtaol cinq hommes de leur famille, des hommes vaillants, pour explorer le pays et le sonder. Ils leur dirent: « Allez, explorez le pays! » Ils arrivèrent dans la montagne d'Ephraïm, à la maison de Mica, et ils y passèrent la nuit.
Saboda haka mutanen Dan suka aika jarumawa guda biyar daga Zora da Eshtawol don su leƙi asirin ƙasar su kuma bincike ta. Waɗannan mutanen sun wakilci dukan kabilar. Suka ce musu, “Ku je, ku bincike ƙasar.” Mutanen suka shiga ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika, inda suka kwana.
3 Lorsqu'ils furent près de la maison de Michée, ils reconnurent la voix du jeune homme, le Lévite; ils s'y rendirent donc et lui dirent: « Qui t'a amené ici? Que fais-tu dans ce lieu? Que possèdes-tu ici? »
Sa’ad da suka yi kusa da gidan Mika, sai suka gane muryar saurayin nan Balawe; saboda haka suka shiga wurin suka tambaye shi, “Wa ya kawo ka nan? Me kake yi a nan? Me ya sa kake a nan?”
4 Il leur dit: « C'est ainsi que Michée m'a traité, il m'a engagé et je suis devenu son prêtre. »
Ya gaya musu abin da Mika ya faɗa masa ya ce, “Ya ɗauke ni aiki ya kuma sa in zama masa firist.”
5 Ils lui dirent: « Je t'en prie, demande conseil à Dieu, afin que nous sachions si la voie que nous suivons sera prospère. »
Sa’an nan suka ce masa, “Muna roƙonka ka nemi mana nufin Allah don mu sani ko tafiyarmu tana da nasara.”
6 Le prêtre leur dit: « Allez en paix. La voie que vous suivez est devant l'Éternel. »
Firist ya amsa ya ce, “Ku sauka lafiya, gama tafiyarku tana da yardan Ubangiji.”
7 Et les cinq hommes partirent, et vinrent à Laïsh, et virent le peuple qui était là, et comment ils vivaient en sécurité, à la manière des Sidoniens, tranquilles et en sûreté; car il n'y avait personne dans le pays qui possédât de l'autorité, qui pût leur faire honte en quoi que ce soit; et ils étaient loin des Sidoniens, et ils n'avaient affaire à personne d'autre.
Saboda haka mutum biyar ɗin suka tashi suka iso Layish, inda suka ga mutane suna zamansu a huce, kamar Sidoniyawa, ba sa zato ga tsaro. Kuma da yake ƙasarsu ba ta bukata kome, suna da wadata. Suna kuma nesa da Sidoniyawa, ba sa kuma hulɗa da kowa.
8 Ils arrivèrent auprès de leurs frères à Zorah et à Eshtaol; et leurs frères leur demandèrent: « Que dites-vous? »
Da suka komo Zora da Eshtawol,’yan’uwansu suka tambaye su, “Me kuka gano?”
9 Ils dirent: « Levez-vous, et montons contre eux; car nous avons vu le pays, et voici, il est très bon. Restez-vous immobiles? Ne soyez pas paresseux pour aller et entrer en possession du pays.
Suka ce, “Ku zo mu yaƙe su! Mun ga ƙasar tana da kyau sosai. Ba za ku yi wani abu ba? Kada ku yi wata-wata, ku je kun mallaki ƙasar.
10 En partant, vous rencontrerez un peuple qui ne se doute de rien, et le pays est vaste, car Dieu l'a remis entre vos mains, un lieu où rien ne manque de ce qui est sur la terre. »
Sa’ad da kun kai can, za ku iske mutanen suna zama a sake, ƙasar kuwa mai faɗi ce wadda Allah ya sa a hannuwanku, ƙasar da ba tă rasa kome ba.”
11 La famille des Danites partit de Zorah et d'Eshtaol, avec six cents hommes armés d'armes de guerre.
Sai mutane ɗari shida daga kabilar Dan suka yi ɗamarar yaƙi, suka tashi daga Zora da Eshtawol.
12 Ils montèrent et campèrent à Kiriath Jearim, en Juda. C'est pourquoi on a appelé ce lieu Mahaneh Dan jusqu'à ce jour. Voici, il est derrière Kirjath Jearim.
A kan hanyarsu suka kafa sansani kusa da Kiriyat Yeyarim a Yahuda. Shi ya sa a ana kira wurin nan yamma da Kiriyat Yeyarim Mahane Dan har wa yau.
13 Ils passèrent de là dans la montagne d'Éphraïm, et arrivèrent à la maison de Michée.
Daga can suka tafi ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika.
14 Les cinq hommes qui étaient allés explorer le pays de Laïsch prirent la parole et dirent à leurs frères: « Savez-vous qu'il y a dans ces maisons un éphod, des théraphim, une image taillée et une image en fonte? Considérez donc maintenant ce que vous avez à faire. »
Sa’an nan mutum biyar ɗin nan da suka leƙi asirin ƙasar Layish suka ce wa’yan’uwansu, “Kun san cewa ɗaya daga cikin gidajen nan yana da efod, waɗansu allolin iyali, siffar da aka sassaƙa da kuma gunki na zubi? To, kun san abin da za ku yi.”
15 Ils passèrent par là, arrivèrent à la maison du jeune Lévite, à la maison de Michée, et lui demandèrent comment il allait.
Saboda haka suka juya a wurin suka shiga gidan saurayin nan Balawe a wajen Mika suka gaishe shi.
16 Les six cents hommes armés de leurs armes de guerre, qui étaient des fils de Dan, se tenaient à l'entrée de la porte.
Mutanen Dan ɗari shida da suka sha ɗamarar yaƙi suka tsaya a bakin ƙofa.
17 Les cinq hommes qui étaient allés explorer le pays montèrent et entrèrent là, et ils prirent l'image taillée, l'éphod, les théraphim et l'image en fonte; le prêtre se tint à l'entrée de la porte avec les six cents hommes armés de fusils de guerre.
Sai mutum biyar da suka leƙi asirin ƙasar suka shiga ciki suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi yayinda firist ɗin tare da mutane ɗari shida da suka yi ɗamarar yaƙi suna tsaye a bakin ƙofa.
18 Lorsque ceux-ci entrèrent dans la maison de Michée et prirent l'image gravée, l'éphod, le théraphim et l'image en fusion, le prêtre leur dit: « Que faites-vous? »
Sa’ad da waɗannan mutane suka shiga gidan Mika suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi, sai firist ya ce musu, “Me kuke yi?”
19 Ils lui dirent: « Tais-toi, mets ta main sur ta bouche, et viens avec nous. Sois pour nous un père et un prêtre. Est-il préférable pour toi d'être prêtre de la maison d'un seul homme, ou d'être prêtre d'une tribu et d'une famille en Israël? ».
Suka ce, “Ka yi shiru! Kada ka ce wani abu. Zo tare da mu, ka zama mahaifinmu da kuma firist. Bai fi maka ka yi wa kabila da kuma zuriya a Isra’ila aikin firist ba, da ka bauta wa iyali guda kawai?”
20 Le cœur du prêtre se réjouit, il prit l'éphod, les théraphim et la statue gravée, et il partit avec le peuple.
Sai firist ya yi farin ciki. Ya ɗauki efod, sauran allolin gida da siffar da aka sassaƙa ya tafi tare da mutanen.
21 Ils se retournèrent et partirent, et mirent devant eux les petits enfants, le bétail et les biens.
Suka sa’ya’yansu ƙanana a gaba, dabbobinsu da mallakansu a gabansu, suka juya suka tafi.
22 Lorsqu'ils furent à bonne distance de la maison de Michée, les hommes qui étaient dans les maisons voisines de la maison de Michée se rassemblèrent et rattrapèrent les fils de Dan.
Sa’ad da suka yi ɗan nisa daga gidan Mika, sai aka kira mutanen da suke maƙwabtakar da Mika suka taru suka bi mutanen Dan suka cim musu.
23 Comme ils appelaient les enfants de Dan, ceux-ci tournèrent le visage et dirent à Michée: « Qu'as-tu, pour venir avec une telle troupe? »
Da suna ihu suna binsu, sai mutanen Dan suka waiga suka cewa Mika, “Mece ce damuwarka da ka kira mutanenka su zo su fāɗa mana?”
24 Il dit: « Tu as pris mes dieux que j'avais faits, ainsi que le prêtre, et tu es parti! Que me reste-t-il? Comment peux-tu me demander: « Qu'est-ce que tu as? »
Ya amsa ya ce, “Kun kwashe allolin da na yi, da kuma firist nawa, kuka tafi. Me kuma nake da shi? Yaya za ku ce, ‘Mece ce damuwata?’”
25 Les enfants de Dan lui dirent: « Ne fais pas entendre ta voix au milieu de nous, de peur que des hommes furieux ne tombent sur toi et que tu ne perdes la vie, avec celle de ta famille. »
Mutanen Dan suka ce, “Kada ka kuskura ka ce kome, in ba haka ba mutanen nan za su harzuƙa, da kai da iyalinka duka ku rasa rayukanku.”
26 Les fils de Dan s'en allèrent; et lorsque Michée vit qu'ils étaient trop forts pour lui, il se retourna et retourna dans sa maison.
Saboda haka mutanen Dan suka kama hanyarsu, Mika kuwa da ya ga an fi ƙarfinsa, sai ya juya ya koma gida.
27 Ils prirent ce que Michée avait fait, et le prêtre qu'il avait, et ils arrivèrent à Laïsh, vers un peuple tranquille et sans méfiance, et ils les frappèrent du tranchant de l'épée; puis ils brûlèrent la ville par le feu.
Sa’an nan suka ɗauko abin da Mika ya yi, da firist nasa, suka tafi Layish, suka fāɗa wa mutanen da suke zaman lafiya, ransu kuma a kwance. Suka fāɗa musu suka kuma ƙone birninsu.
28 Il n'y avait pas de libérateur, car elle était loin de Sidon, et ils n'avaient affaire à personne d'autre; elle était dans la vallée qui s'étend près de Beth Rehob. Ils bâtirent la ville et l'habitèrent.
Ba wanda zai cece su domin suna nesa da Bet-Sidon kuma ba sa hulɗa da kowa. Birnin yana a kwari kusa da Bet-Rekob. Mutanen Dan suka sāke gina birnin suka zauna a can.
29 Ils appelèrent le nom de la ville Dan, d'après le nom de Dan, leur père, qui était né en Israël; cependant le nom de la ville était autrefois Laish.
Suka sa wa birnin suna Dan, wato, sunan kakansu Dan, wanda aka haifa wa Isra’ila, ko da yake a dā ana kira birnin Layish.
30 Les fils de Dan s'établirent l'image taillée; et Jonathan, fils de Gershom, fils de Moïse, et ses fils, furent prêtres pour la tribu des Danites jusqu'au jour de la captivité du pays.
A can mutanen Dan suka kafa wa kansu gumaka, Yonatan ɗan Gershom, ɗan Musa, da’ya’yansa maza firistoci ne na kabilar Dan har lokacin da aka kwashe mutane zuwa bauta.
31 Et ils s'établirent l'image taillée de Michée, qu'il avait faite, et elle resta tout le temps que la maison de Dieu fut à Silo.
Suka ci gaba da amfani da gumakan da Mika ya yi, a duk wannan lokacin gidan Allah yana a Shilo.

< Juges 18 >