< Juges 15 >

1 Mais au bout de quelque temps, au moment de la moisson des blés, Samson rendit visite à sa femme avec un chevreau. Il dit: « Je vais entrer dans la chambre de ma femme. » Mais son père ne lui permit pas d'entrer.
Daga baya, a lokacin girbin alkama, Samson ya ɗauki ɗan akuya ya tafi yă ziyarci matarsa. Sai ya ce, “Zan in shiga ɗakin matata.” Amma mahaifinta ya hana shi shiga.
2 Son père dit: « J'ai bien cru que tu la détestais; c'est pourquoi je l'ai donnée à ton compagnon. Sa jeune sœur n'est-elle pas plus belle qu'elle? S'il te plaît, prends-la à sa place. »
Ya ce wa, “Na tabbata ba ka sonta sam-sam, don haka na ba da ita ga abokinka. Ba ƙanuwarta ta fi kyau ba? Ka ɗauke ta a maimako.”
3 Samson leur dit: « Cette fois, je serai irréprochable à l'égard des Philistins quand je leur ferai du mal. »
Samson kuwa ya ce musu, “A wannan lokaci ina da iko in rama a kan Filistiyawa; tabbatacce zan ji musu.”
4 Samson alla attraper trois cents renards, prit des torches, tourna la queue contre la queue et mit une torche au milieu entre deux queues.
Saboda haka ya tafi ya kama yanyawa ɗari uku ya ɗaura wutsiyoyinsu wutsiya da wutsiya. Sa’an nan ya daure acibalbal a tsakanin ko waɗanne wutsiya biyu,
5 Quand il eut mis le feu aux torches, il les lança dans le blé sur pied des Philistins, et brûla tant les chocs que le blé sur pied, et aussi les oliviers.
sai ya sa wa acibalbal wuta, ya saki yanyawan suka shiga gonakin Filistiyawa. Suka ƙone dammunan hatsi da hatsin da yake tsaye, tare da gonakin inabi da na zaitun.
6 Alors les Philistins dirent: « Qui a fait cela? » Ils dirent: « Samson, le gendre du Timnite, car il a pris sa femme et l'a donnée à son compagnon. » Les Philistins montèrent, et la brûlèrent au feu, elle et son père.
Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Wane ne ya yi wannan abu?” Sai aka ce musu, “Ai, Samson ne surukin mutumin Timna, domin an ba wa abokinsa matarsa.” Saboda haka Filistiyawa suka haura suka je suka ƙone ta da mahaifinta ƙurmus da wuta.
7 Samson leur dit: « Si vous vous comportez ainsi, je me vengerai de vous, et après cela je cesserai. »
Samson ya ce musu, “Tun da kun aikata wannan, ba zan bari ba har sai na ɗau fansa a kanku.”
8 Il les frappa de la hanche et de la cuisse avec un grand coup de massue; puis il descendit et habita dans la caverne du rocher d'Etam.
Ya kuwa fāɗa musu ya kuma karkashe su da yawa. Sa’an nan ya gangara ya zauna a kogo a dutsen Etam.
9 Et les Philistins montèrent, campèrent en Juda, et se répandirent à Léhi.
Filistiyawa suka haura suka yi sansani a Yahuda, suka bazu kusa da Lehi.
10 Les hommes de Juda dirent: « Pourquoi êtes-vous venus contre nous? » Ils ont dit: « Nous sommes montés pour lier Samson, pour lui faire ce qu'il nous a fait. »
Mutanen Yahuda suka ce, “Me ya sa kuka zo mana da yaƙi?” Sai suka ce, “Mun zo ne mu kama Samson, a matsayin fursunan yaƙi, mu yi masa kamar yadda ya yi mana.”
11 Et trois mille hommes de Juda descendirent à la grotte du rocher d'Etam et dirent à Samson: « Ne sais-tu pas que les Philistins nous dominent? Qu'est-ce donc que tu nous as fait? » Il leur a dit: « Ce qu'ils m'ont fait, je le leur ai fait. »
Sa’an nan mutane dubu uku daga Yahuda suka gangara wajen Samson a kogo a dutsen Etam. Suka ce masa, “Ba ka san cewa Filistiyawa ne suke mulkinmu ba? Me ke nan ka yi mana?” Ya ce musu, “Na ɗan yi musu abin da suka yi mini ne.”
12 Ils lui dirent: « Nous sommes descendus pour te lier, afin de te livrer entre les mains des Philistins. » Samson leur a dit: « Jurez-moi que vous ne m'attaquerez pas vous-mêmes. »
Suka ce masa, “To, mun zo ne mu daure ka mu kai wa Filistiyawa.” Samson ya ce, “Ku rantse mini ba za ku kashe ni da kanku ba.”
13 Ils lui dirent: « Non, mais nous te lierons solidement et nous te livrerons entre leurs mains; mais sûrement nous ne te tuerons pas. » Ils le lièrent avec deux cordes neuves, et le firent remonter du rocher.
Suka ce, “Mun yarda, za mu dai daure ka mu ba da kai gare su. Ba za mu kashe ka ba.” Saboda haka suka daure shi da sababbin igiyoyi biyu, suka saukar da shi daga dutsen.
14 Lorsqu'il arriva à Léhi, les Philistins poussèrent des cris de joie en le rencontrant. Alors l'Esprit de Yahvé vint puissamment sur lui, et les cordes qui étaient à ses bras devinrent comme du lin brûlé au feu, et ses ceintures tombèrent de ses mains.
Yayinda ya zo gab da Lehi, sai Filistiyawa suka sheƙo a guje da ihu suka nufo shi. Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko da iko a kansa. Igiyoyin da suke daure a hannuwansa kuwa suka zama kamar abin da wuta ta babbaka, suka tsintsinke suka zuba daga hannuwansa.
15 Il trouva une mâchoire fraîche d'un âne, étendit la main, la prit et en frappa mille hommes.
Da ya samo muƙamuƙin jaki, ya ɗauka, sai ya karkashe mutane dubu ɗaya.
16 Samson dit: « Avec la mâchoire d'un âne, des monceaux de monceaux, avec la mâchoire d'un âne, j'ai frappé mille hommes. »
Sa’an nan Samson ya ce, “Da muƙamuƙin jaki na mai da su jakuna. Da muƙamuƙin jaki na kashe mutum dubu.”
17 Quand il eut fini de parler, il jeta la mâchoire de sa main; et ce lieu fut appelé Ramath Léhi.
Da ya gama magana, sai ya jefar da muƙamuƙin; aka ba wa wannan wuri suna Ramat Lehi.
18 Il avait très soif, et il invoqua Yahvé en disant: « Tu as accordé cette grande délivrance par la main de ton serviteur; et maintenant, vais-je mourir de soif, et tomber entre les mains des incirconcis? »
Saboda ƙishirwa ta kama shi ƙwarai, sai ya ce wa Ubangiji, “Ka ba bawanka wannan babbar nasara. To, sai in mutu da ƙishirwa, har in shiga a hannun marasa kaciyan nan su kashe ni?”
19 Mais Dieu fendit le creux qui est à Léhi, et il en sortit de l'eau. Quand il eut bu, son esprit revint, et il revint à la vie. C'est pourquoi on l'a appelé jusqu'à ce jour En Hakkore, qui est à Léhi.
Sa’an nan Allah ya buɗe wani rami a Lehi, ruwa kuwa ya fito daga ciki. Da Samson ya sha, sai ƙarfinsa ya dawo, ya kuma wartsake. Aka sa wa wannan maɓulɓula suna En Hakkore, yana nan a Lehi har wa yau.
20 Il jugea Israël pendant vingt ans, au temps des Philistins.
Samson kuwa ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin a zamanin Filistiyawa.

< Juges 15 >