< Juges 14 >
1 Samson descendit à Thimna, et il vit à Thimna une femme d'entre les filles des Philistins.
Samson ya gangara zuwa Timna a can ya ga wata daga cikin’yan mata Filistiyawa.
2 Il remonta, et le rapporta à son père et à sa mère, en disant: « J'ai vu à Thimna une femme d'entre les filles des Philistins. Maintenant, prends-la pour moi comme femme. »
Da ya komo, sai ya gaya wa mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, “Na ga wata mace a Timna; ku auro mini ita ta zama matata.”
3 Et son père et sa mère lui dirent: « N'y a-t-il pas une femme parmi les filles de tes frères, ou parmi tout mon peuple, que tu ailles prendre une femme chez les Philistins incirconcis? » Samson dit à son père: « Prends-la pour moi, car elle me plaît bien. »
Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka ce, “Babu wata karɓaɓɓiyar yarinya a cikin zuriyarku ko cikin dukan mutanenmu ne? Dole ne ka tafi wajen Filistiyawa marasa kaciya ka nemi aure?” Amma Samson ya ce wa mahaifinsa, “A auro mini ita dai. Ita ta dace da ni.”
4 Mais son père et sa mère ne savaient pas que c'était de la part de l'Éternel, car il cherchait une occasion de se battre contre les Philistins. Or, en ce temps-là, les Philistins dominaient sur Israël.
(Iyayensa ba su san cewa wannan daga wurin Ubangiji ne ba, wanda yake neman hanyar da za a kai wa Filistiyawa hari; gama a lokacin suna mulkin Isra’ila.)
5 Alors Samson descendit à Thimna avec son père et sa mère, et il arriva dans les vignes de Thimna; et voici qu'un jeune lion rugit contre lui.
Sai Samson ya gangara zuwa Timna tare da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa. Da suka yi kusa da gonar inabin Timna, nan da nan sai ga ɗan zaki ya taso ya nufe shi yana ruri.
6 L'Esprit de Yahvé vint puissamment sur lui, et il le déchira comme il aurait déchiré un chevreau à mains nues, mais il ne dit pas à son père ni à sa mère ce qu'il avait fait.
Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko masa da ƙarfi, ya sa ya yaga zakin kashi biyu da hannu kamar yadda akan yayyage ɗan akuya. Sai dai bai gaya wa iyayensa abin da ya yi ba.
7 Il descendit et parla avec la femme, et elle plut à Samson.
Sa’an nan ya gangara ya yi magana da yarinyar, yana kuwa sonsa.
8 Au bout d'un moment, il revint la chercher, et il alla voir le cadavre du lion; et voici, il y avait un essaim d'abeilles dans le cadavre du lion, et du miel.
Daga baya, da ya koma don yă aure ta, sai ya ratse don yă ga gawar zakin. Sai ga taron ƙudan zuma da zuma a ciki,
9 Il le prit dans ses mains, et s'en alla, mangeant en chemin. Il vint vers son père et sa mère et leur donna, et ils mangèrent, mais il ne leur dit pas qu'il avait pris le miel dans le corps du lion.
wanda ya sa hannu ya ɗebo yana tafiya yana sha. Sa’ad da ya iso wurin iyayensa, ya ba su zuman, su ma suka sha. Sai dai bai gaya musu cewa ya ɗebo zuman daga gawar zaki ba.
10 Son père descendit chez la femme, et Samson y fit un festin, car les jeunes gens ont l'habitude de le faire.
To, mahaifinsa ya gangara don yă ga yarinyar. Samson kuwa ya shirya wata liyafa a can, yadda yake bisa ga al’adar angwaye.
11 Quand ils le virent, ils amenèrent trente compagnons pour être avec lui.
Sa’ad da ya bayyana, sai aka haɗa shi abokai talatin.
12 Samson leur dit: « Je vais vous poser une énigme. Si vous pouvez me donner la réponse dans les sept jours de la fête et la découvrir, alors je vous donnerai trente vêtements de lin et trente vêtements de rechange;
Sai Samson ya ce, “Bari in yi muku kacici-kacici, in kun ba ni amsa cikin kwana bakwai na wannan biki, zan ba ku riguna lilin talatin da kuma tufafi talatin.
13 mais si vous ne pouvez pas me donner la réponse, alors vous me donnerez trente vêtements de lin et trente vêtements de rechange. » Ils lui dirent: « Dis-nous ton énigme, afin que nous l'entendions. »
In kuma ba ku iya ba ni amsar ba, dole ku ba ni rigunan lilin talatin da tufafi talatin.” Suka ce, “Ka gaya mana kacici-kacicin.”
14 Il leur dit, « Du mangeur est sortie la nourriture. De la force est sortie la douceur. » En trois jours, ils n'ont pas pu résoudre l'énigme.
Sai ya ce, “Daga mai ci, abinci ya fito; daga mai ƙarfi, abu mai zaki ya fito.” Har kwana uku ba su iya ba da amsa ba.
15 Le septième jour, ils dirent à la femme de Samson: « Attire ton mari pour qu'il nous révèle l'énigme, de peur que nous ne te brûlions, toi et la maison de ton père. Nous avez-vous appelés pour nous appauvrir? N'est-ce pas? »
A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson “Ki rarrashi mijinki yă bayyana mana kacici-kacicin, ko kuwa mu ƙone ki da gidan mahaifinki duka da wuta. Kun kira mu domin ku yi mana fashi ne?”
16 La femme de Samson pleura devant lui et dit: « Tu me hais et tu ne m'aimes pas. Tu as raconté une énigme aux enfants de mon peuple, et tu ne l'as pas racontée à moi. » Il lui dit: « Voici, je ne l'ai dit ni à mon père ni à ma mère, alors pourquoi devrais-je te le dire? ».
Sa’an nan matar Samson ta kwanta masa a jiki tana kuka tana cewa, “Kai maƙiyina ne, lalle ba ka ƙaunata, ka yi wa mutanena kacici-kacici, amma ba ka gaya mini amsar ba.” Ya amsa ya ce, “Ban ma bayyana wa mahaifina ko mahaifiyata ba, to, don me zan bayyana miki?”
17 Elle pleura devant lui les sept jours que dura leur fête; et le septième jour, il le lui dit, car elle le pressait durement; et elle raconta l'énigme aux enfants de son peuple.
Ta yi ta kuka har kwana bakwai na bikin. Saboda haka a rana ta bakwai sai ya gaya mata, don ta dame shi. Ita kuwa ta bayyana kacici-kacicin wa mutanenta.
18 Le septième jour, avant le coucher du soleil, les hommes de la ville lui dirent: « Qu'est-ce qui est plus doux que le miel? Qu'est-ce qui est plus fort qu'un lion? » Il leur a dit, « Si tu n'avais pas labouré avec ma génisse, vous n'auriez pas découvert mon énigme. »
Kafin rana ta fāɗi a rana ta bakwai mutane garin suka ce masa, “Me ya fi zuma zaki? Me ya fi zaki ƙarfi?” Samson ya ce musu, “Da ba don kun haɗa baki da matata ba, da ba za ku san amsar kacici-kacici ba.”
19 L'Esprit de Yahvé se manifesta puissamment sur lui, il descendit à Ashkelon et en frappa trente hommes. Il prit leur butin, puis donna les vêtements de rechange à ceux qui avaient déclaré l'énigme. Sa colère s'enflamma, et il monta à la maison de son père.
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko masa da iko. Sai ya fita ya gangara zuwa Ashkelon, ya kashe mutanensu talatin, ya kwashe kayansu ya kuma ba da rigunarsu ga waɗanda suka bayyana kacici-kacicin. Cike da fushi, ya haura zuwa gidan mahaifinsa.
20 Mais la femme de Samson fut donnée à son compagnon, qui avait été son ami.
Aka kuma ɗauki matar Samson aka ba wa ɗaya daga cikin waɗanda suka yi masa hidima a bikin.