< Juges 13 >

1 Les enfants d'Israël firent encore ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, et l'Éternel les livra entre les mains des Philistins pendant quarante ans.
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda haka ya ba da su a hannun Filistiyawa shekara arba’in.
2 Il y avait un homme de Tsorea, de la famille des Danites, dont le nom était Manoach; sa femme était stérile et sans enfants.
Akwai wani mutumin Zora, mai suna Manowa, daga kabilar Dan, matarsa kuwa bakararriya ce, ba ta haihuwa.
3 L'ange de Yahvé apparut à la femme et lui dit: « Voici, tu es stérile et sans enfants; mais tu concevras et tu enfanteras un fils.
Mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare ta ya ce, “Ga shi ke bakararriya ce ba kya haihuwa, amma za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa.
4 Maintenant, prends garde, ne bois pas de vin ni de boisson forte, et ne mange pas de choses impures;
To, sai ki lura kada ki sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye, kada kuma ki ci wani abu marar tsarki,
5 car voici, tu concevras et tu enfanteras un fils. Aucun rasoir ne viendra sur sa tête, car l'enfant sera naziréen à Dieu dès le ventre de sa mère. C'est lui qui commencera à sauver Israël de la main des Philistins. »
gama za ki yi ciki, ki haifi ɗa. Aska ba za tă taɓa kansa ba, domin yaron zai zama Banazare, keɓaɓɓe ga Allah tun daga haihuwa, shi ne kuwa zai soma ceton Isra’ilawa daga hannuwan Filistiyawa.”
6 Alors la femme vint le dire à son mari, en disant: « Un homme de Dieu est venu à moi, et son visage était comme celui de l'ange de Dieu, très impressionnant. Je ne lui ai pas demandé d'où il venait, et il ne m'a pas dit son nom;
Sa’an nan matar ta tafi wajen mijinta ta faɗa masa cewa, “Wani mutumin Allah ya zo wurina. Ya yi kama da mala’ikan Allah, yana da bantsoro ƙwarai. Ban tambaye shi inda ya fito ba, kuma bai gaya mini sunansa ba.
7 mais il m'a dit: 'Voici que tu vas concevoir et enfanter un fils; et maintenant ne bois ni vin ni boisson forte. Ne mange pas de choses impures, car l'enfant sera naziréen pour Dieu depuis le ventre de sa mère jusqu'au jour de sa mort.'"
Sai dai ya ce mini, ‘Za ki yi ciki, ki kuma haifi ɗa. To, fa, kada ki sha ruwan inabi ko abu mai sa maye kada kuma ki ci abin da yake marar tsarki, gama ɗan zai zama Banazare na Allah tun daga haihuwa har ranar mutuwarsa.’”
8 Alors Manoah pria Yahvé et dit: « Oh, Seigneur, fais que l'homme de Dieu que tu as envoyé revienne vers nous, et qu'il nous apprenne ce que nous devons faire à l'enfant qui va naître. »
Sai Manowa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, bari mutumin Allahn da ka aiko mana yă sāke zuwa don yă koya mana yadda za mu goyi yaron da za a haifa.”
9 Dieu écouta la voix de Manoah, et l'ange de Dieu revint vers la femme comme elle était assise dans les champs; mais Manoah, son mari, n'était pas avec elle.
Allah ya ji Manowa, sai mala’ikan Allah ya sāke zuwa wurin matar yayinda take gona; amma Manowa mijinta ba ya tare da ita.
10 La femme se hâta et courut le dire à son mari, en lui disant: « Voici que l'homme qui m'était apparu ce jour-là m'est apparu. »
Sai matar ta ruga don ta faɗa wa mijinta, ta ce, “Ga shi ya zo! Mutumin da ya bayyana mini ran nan!”
11 Manoah se leva et suivit sa femme; il vint vers l'homme et lui dit: « Es-tu l'homme qui a parlé à ma femme? » Il a dit: « Je le suis. »
Manowa ya tashi ya bi matarsa. Da ya zo wurin mutumin, sai ya ce, “Kai ne wanda ka yi magana da matata?” Ya ce, “Ni ne.”
12 Manoah dit: « Que tes paroles se réalisent maintenant. Quel sera le mode de vie et la mission de l'enfant? »
Saboda haka Manowa ya tambaye shi ya ce, “Sa’ad da maganarka ta cika, me za tă zama dokar rayuwar yaron da kuma aikinsa?”
13 L'ange de Yahvé dit à Manoah: « Qu'elle prenne garde à tout ce que j'ai dit à la femme.
Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Dole matarka ta kiyaye duk abin da na riga na gaya mata.
14 Qu'elle ne mange pas de ce qui vient de la vigne, qu'elle ne boive pas de vin ni de boisson forte, et qu'elle ne mange aucune chose impure. Qu'elle observe tout ce que je lui ai ordonné. »
Kada tă ci kowane iri abin da ya fito daga inabi, ba kuwa za tă sha ruwan inabi, ko abu mai sa maye ko ta ci abu marar tsarki ba. Dole tă kiyaye duk abin da na umarce mata.”
15 Manoah dit à l'ange de l'Yahvé: « Reste avec nous, je te prie, afin que nous préparions un chevreau pour toi. »
Manowa ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Muna roƙonka ka jira mu yanka maka ɗan akuya.”
16 L'ange de Yahvé dit à Manoah: « Si tu me retiens, je ne mangerai pas ton pain. Si tu veux préparer un holocauste, tu dois l'offrir à Yahvé. » Car Manoah ne savait pas que c'était l'ange de Yahvé.
Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ko kun sa na tsaya, ba zan ci abincinku ba. Amma in kun shirya hadaya ta ƙonawa, ku miƙa wa Ubangiji.” (Manowa bai gane cewa mala’ikan Ubangiji ne ba.)
17 Manoah dit à l'ange de Yahvé: « Quel est ton nom, afin que, lorsque tes paroles se réaliseront, nous puissions t'honorer? »
Sa’an nan Manowa ya sāke tambayi mala’ikan Ubangiji ya ce, “Mene ne sunanka, don mu girmama ka sa’ad da maganarka ta tabbata.”
18 L'ange de Yahvé lui dit: « Pourquoi demandes-tu mon nom, puisqu'il est incompréhensible? »
Ya ce, “Me ya sa kake tambaya sunana? Ai, ya wuce fahimta.”
19 Manoah prit le chevreau avec l'offrande et l'offrit sur le rocher à Yahvé. Et l'ange fit une chose étonnante, sous le regard de Manoah et de sa femme.
Sa’an nan Manowa ya ɗauki ɗan akuya, tare da hadaya ta hatsi ya miƙa wa Ubangiji a kan dutse. Ubangiji kuwa ya yi abin mamaki yayinda Manowa da matarsa suke kallo.
20 Car lorsque la flamme de l'autel s'éleva vers le ciel, l'ange de Yahvé monta dans la flamme de l'autel. Manoah et sa femme regardaient, et ils tombèrent la face contre terre.
Yayinda harshen wuta ya yi sama daga bagaden, sai mala’ikan Ubangiji ya haura cikin harshen wutar. Da ganin wannan Manowa da matarsa suka fāɗi da fuskokinsu har ƙasa.
21 Mais l'ange de Yahvé n'apparut plus ni à Manoah ni à sa femme. Alors Manoah sut que c'était l'ange de Yahvé.
Da mala’ikan Ubangiji bai ƙara bayyana kansa ga Manowa da matarsa ba, sai Manowa ya gane cewa mala’ikan Ubangiji ne.
22 Manoah dit à sa femme: « Nous allons mourir, car nous avons vu Dieu. »
Ya ce wa matar, “Ba shakka za mu mutu, gama mun ga Allah!”
23 Mais sa femme lui dit: « Si Yahvé voulait nous tuer, il n'aurait pas reçu de notre part un holocauste et une offrande de repas, et il ne nous aurait pas montré toutes ces choses, et il ne nous aurait pas dit de telles choses en ce moment. »
Amma matar ta ce, “Da Ubangiji yana nufin kashe mu ne, da ba zai karɓi hadaya ta ƙonawa da hadaya ta hatsi daga hannunmu, ko yă nuna mana dukan waɗannan abubuwa ko abin da ya gaya mana ba.”
24 La femme enfanta un fils et le nomma Samson. L'enfant grandit, et Yahvé le bénit.
Matar kuwa ta haifi ɗa, aka sa masa suna Samson. Ya yi girma Ubangiji kuma ya albarkace shi,
25 L'Esprit de Yahvé commença à le toucher à Mahaneh Dan, entre Zorah et Eshtaol.
Ruhun Ubangiji kuwa ya fara iza shi yayinda yake a Mahane Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.

< Juges 13 >