< Josué 1 >

1 Après la mort de Moïse, serviteur de Yahvé, Yahvé parla à Josué, fils de Nun, serviteur de Moïse, en disant:
Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
2 « Moïse, mon serviteur, est mort. Maintenant, lève-toi, passe ce Jourdain, toi et tout ce peuple, pour aller dans le pays que je vais leur donner, aux enfants d'Israël.
“Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
3 Je vous ai donné tous les lieux que la plante de votre pied pourra fouler, comme je l'ai dit à Moïse.
Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
4 Depuis le désert et ce Liban jusqu'au grand fleuve, le fleuve Euphrate, tout le pays des Héthiens, et jusqu'à la grande mer vers le coucher du soleil, telle sera votre frontière.
Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
5 Aucun homme ne pourra se tenir devant toi tous les jours de ta vie. Comme j'ai été avec Moïse, je serai avec toi. Je ne te laisserai pas tomber et je ne t'abandonnerai pas.
Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
6 « Sois fort et courageux, car tu feras en sorte que ce peuple hérite du pays que j'ai juré à ses pères de lui donner.
“Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
7 Seulement, soyez forts et très courageux. Prends soin d'observer et de faire selon toute la loi que Moïse, mon serviteur, t'a prescrite. Ne vous en détournez ni à droite ni à gauche, afin que vous ayez du succès partout où vous irez.
Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
8 Ce livre de la loi ne s'éloignera pas de ta bouche, mais tu le méditeras jour et nuit, afin d'observer et de mettre en pratique tout ce qui y est écrit; car c'est alors que tu feras prospérer ton chemin, et c'est alors que tu auras du succès.
Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
9 Ne t'ai-je pas ordonné? Sois fort et courageux. N'aie pas peur. Ne t'effraie pas, ne t'effraie pas, car Yahvé ton Dieu est avec toi partout où tu iras. »
Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
10 Alors Josué donna cet ordre aux officiers du peuple:
Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
11 « Passez au milieu du camp et donnez cet ordre au peuple: « Préparez des vivres, car dans trois jours vous passerez ce Jourdain pour entrer en possession du pays dont Yahvé votre Dieu vous donne la propriété. »"
“Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
12 Josué parla aux Rubénites, aux Gadites et à la demi-tribu de Manassé, et dit:
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
13 « Souvenez-vous de la parole que Moïse, serviteur de Yahvé, vous a prescrite, en disant: « Yahvé, votre Dieu, vous donne du repos et vous donne ce pays.
“Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
14 Vos femmes, vos petits enfants et vos troupeaux vivront dans le pays que Moïse vous a donné de l'autre côté du Jourdain; mais vous passerez devant vos frères en armes, tous les vaillants hommes, et vous les aiderez
Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
15 jusqu'à ce que Yahvé ait donné à vos frères du repos, comme il vous en a donné, et qu'ils aient aussi possédé le pays que Yahvé votre Dieu leur donne. Alors tu retourneras dans le pays qui t'appartient et tu le posséderas, celui que Moïse, serviteur de Yahvé, t'a donné au-delà du Jourdain, vers le lever du soleil.'"
har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
16 Ils répondirent à Josué en disant: « Nous ferons tout ce que tu nous as ordonné, et nous irons partout où tu nous enverras.
Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
17 De même que nous avons écouté Moïse en toutes choses, de même nous t'écouterons. Seulement, que Yahvé ton Dieu soit avec toi, comme il a été avec Moïse.
Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
18 Quiconque se rebellera contre ton commandement, et n'écoutera pas tes paroles dans tout ce que tu lui ordonneras, sera lui-même mis à mort. Seulement, sois fort et courageux. »
Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”

< Josué 1 >